Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, ya ba da umarnin ɗaukar matakan gaggawa domin ƙara tsaro a Cibiyar Nazarin Manufofi da Dabarun Ƙasa (NIPSS) da ke Kuru a Jihar Filato, bayan harin da ’yan bindiga suka kai inda suka kashe sojoji biyu da jami’in ɗansanda ɗaya.
Yayin wata ziyara da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya kai cibiyar a madadin shugaban ƙasa ranar Juma’a, ya miƙa sakon ta’aziyyar gwamnatin tarayya ga iyalan jami’an tsaron da suka rasa rayukansu, tare da tabbatar musu da cewa gwamnati za ta kula da su.
Shettima ya ce Shugaba Tinubu ya umarci mahukuntan NIPSS da su haɗa kai da rundunar sojoji, ’yansanda da DSS domin ƙara tsaro a cibiyar cikin gaggawa.
Ya kuma ce dole ne a gabatar da cikakken shirin inganta tsaro, wanda ya haɗa da sa ido ta na’urori, ƙarin jami’an tsaro, kula da hanyoyin shiga da tsarin gaggawa cikin sa’o’i 72.
Mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana NIPSS a matsayin muhimmiyar cibiyar ƙasa, yana mai cewa kare ta ya zama wajibi ga tsaron Nijeriya.
Ya tabbatar wa ma’aikata da mahalarta shirin cewa tsaronsu na da muhimmanci ga gwamnati, tare da alƙawarin cewa iyalan jami’an tsaron da suka mutu za su samu cikakken tallafi.
Shettima ya kuma yaba wa Darakta Janar na NIPSS, Ayo Omotayo, da sauran jami’an cibiyar bisa yadda suka ɗauki matakan gaggawa wanda ya taimaka wajen tabbatar da tsaro da kare rayukan ma’aikata da mahalarta shirin.
A nasa ɓangaren, Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya amince da ɗaukar wasu matakan inganta tsaro a kewayen cibiyar, ciki har da samar da yankin kariya da kuma girka fitilun tsaro.
Haka kuma, mahukuntan NIPSS sun buƙaci ƙarin jami’an tsaro da na’urorin sa ido kamar kyamarorin CCTV domin ƙara kare cibiyar daga duk wani hari a nan gaba.














Discussion about this post