ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

by Sadiq
2 days ago

Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, ya ba da umarnin ɗaukar matakan gaggawa domin ƙara tsaro a Cibiyar Nazarin Manufofi da Dabarun Ƙasa (NIPSS) da ke Kuru a Jihar Filato, bayan harin da ’yan bindiga suka kai inda suka kashe sojoji biyu da jami’in ɗansanda ɗaya.

Yayin wata ziyara da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya kai cibiyar a madadin shugaban ƙasa ranar Juma’a, ya miƙa sakon ta’aziyyar gwamnatin tarayya ga iyalan jami’an tsaron da suka rasa rayukansu, tare da tabbatar musu da cewa gwamnati za ta kula da su.

Shettima ya ce Shugaba Tinubu ya umarci mahukuntan NIPSS da su haɗa kai da rundunar sojoji, ’yansanda da DSS domin ƙara tsaro a cibiyar cikin gaggawa.

ADVERTISEMENT

Ya kuma ce dole ne a gabatar da cikakken shirin inganta tsaro, wanda ya haɗa da sa ido ta na’urori, ƙarin jami’an tsaro, kula da hanyoyin shiga da tsarin gaggawa cikin sa’o’i 72.

Mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana NIPSS a matsayin muhimmiyar cibiyar ƙasa, yana mai cewa kare ta ya zama wajibi ga tsaron Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

Ya tabbatar wa ma’aikata da mahalarta shirin cewa tsaronsu na da muhimmanci ga gwamnati, tare da alƙawarin cewa iyalan jami’an tsaron da suka mutu za su samu cikakken tallafi.

Shettima ya kuma yaba wa Darakta Janar na NIPSS, Ayo Omotayo, da sauran jami’an cibiyar bisa yadda suka ɗauki matakan gaggawa wanda ya taimaka wajen tabbatar da tsaro da kare rayukan ma’aikata da mahalarta shirin.

A nasa ɓangaren, Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya amince da ɗaukar wasu matakan inganta tsaro a kewayen cibiyar, ciki har da samar da yankin kariya da kuma girka fitilun tsaro.

Haka kuma, mahukuntan NIPSS sun buƙaci ƙarin jami’an tsaro da na’urorin sa ido kamar kyamarorin CCTV domin ƙara kare cibiyar daga duk wani hari a nan gaba.

MASU ALAKA

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar
Manyan Labarai

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi
Manyan Labarai

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni
Manyan Labarai

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Next Post
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.