ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ya Soki Tinubu Kan Ayyana Dokar Ta-ɓaci a Jihar Ribas

by Sadiq
1 year ago
Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki Shugaba Bola Tinubu kan ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, yana mai cewa hakan siyasa ce tsantsa kuma ɓaga dimokuraɗiyya.

Atiku, cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana matakin a matsayin wata maƙarƙashiya ta siyasa da aka yi da mugun nufi.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]
  • Dabarun Kasar Sin Na Iya Kawo Karshen Yunwa A Duniya

Ya zargi Shugaba Tinubu da haddasa rikicin da ke faruwa a Jihar Ribas, ko dai ta hanyar goyon baya ko kuma ƙin ɗaukar matakin daƙile rikicin.

ADVERTISEMENT

A cewar Atiku, idan an lalata kadarorin gwamnatin tarayya a jihar, to Shugaban Ƙasa ne ya kamata ya ɗauki alhakin hakan, ba wai a azabtar da al’ummar Ribas da dokar ta-ɓaci ba.

“Ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas siyasa ce kawai, ba don amfanin jama’a ba. Tinubu na da hannu a rikicin kuma ya kasa ɗaukar matakin da ya kamata. Ƙin ɗaukar matakin da ya yi abin kunya ne,” in ji Atiku.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Ya ƙara da cewa rikicin da ke faruwa a yankin Neja Delta a ƙarƙashin shugabancin Tinubu ya rusa zaman lafiyan da aka samu a zamanin marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua.

Atiku ya jaddada cewa wannan ba batun tsaro ba ne, illa dai wata hanyar wasa da siyasa tsakanin masu goyon bayan Tinubu da Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara.

Ya buƙaci ‘yan Nijeriya su yi Allah-wadai da wannan mataki da ya kira hari kan dimokuraɗiyya.

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
WSCIJ Ta Naɗa Farfesa Umaru Pate A Kwamitin Amintattu

WSCIJ Ta Naɗa Farfesa Umaru Pate A Kwamitin Amintattu

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.