ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AUREN DA NAKE BURI

by Sulaiman
4 years ago

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Fili na musamman domin matasa, wanda yake bawa ku masu karatu dama ku bayyana irin mace ko namijin da kuke son aura, tare da bayyana irin shagalin bikin da kuke son a yi muku, har ma da irin zaman auren da kuke son yi da masoyan naku. A yau ma ina tafe da wasu sakonnin naku kamar haka:

‘Zabina Shi Ne Namiji Dogo Fari Bugun Abuja’
Ni akan kaina ina son namiji dogo fari irin bugun Abuja kun dai gane, wanda kana kallonsa ka san daga cikin AC ya fito, kyakkyawa dan Beauty, mara jiki amma ba siriri ba, dan matsakaici, me dan kauri kadan, wanda kallonsa zai kasance kamar kallon soyayya, me kwantaccen gashin fuska wato saje da kuma gemu kwantacce kadan ba me yawa ba, wanda bakinsa yake dai-dai misali dan tsuwit gwanin birgewa, sannan dan gayu me saka kananan kaya dan ba na son manyan kaya ko zai saka ya zamo iya juma’a ce kawai ko kuma zuwa sallar idi ko wajen daurin aure, Allah ka ba ni. To fa irin auren da nake buri ai ni kowanne ne ma ya samu ina so muddin zan samu irin wanda na lissafo. Zaman auren da za mu yi, za mu yi rayuwar jin dadi ta birgewa, irin wadda ba za mu so mu rabu da juna ba, duk wani aiki da zan yi tare za mu yi, wajen aiki ma in da hali na bishi na zauna gefe in ya gama mu taho tare.
Daga Suhailat Idris Jihar Bauchi

‘Ina Son Namijin Da Ba Zan Ji Kunyar Shiga Da Shi Ko Ina Ba’
Auren da nake buri ina son na auri namiji Dan gayu wanda ba zan ji kunyar shiga da shi ko’ina ba, ban damu da fari ne shi ko baki, mai kiba ko akasin haka ba, kawai burina ya kasance Dan gayu, sannan ina son ya kasance mai kwalliya, amma fa babban mutum irin 60yrs din nan, wanda zai rinka riritani tamkar kwai akan cokali, wanda zai so ni kamar ya mai da ni cikinsa ya girmama iyayena tamkar su suka haife shi, ya aje ni a Lagos saboda mu rinka ziyartar tekuna, saboda ina son na ganni ni da shi a gabar ruwa na san wannan yanayin zai mana dadi sosai, amma fa ni ba zan zauna gida daya da matarsa ba ko yaransa ba.
Daga Hussy Saniey

ADVERTISEMENT

‘Na Zabi Namiji Mara Girman Kai A Matsayin Miji’
Burina shi ne na auri namijin da ba shida girman kai, wanda in ya yi ba dai-dai ba matarsa ta yi masa gyara zai yarda da wannan gyaran da ta yi masa, Ina son namiji mai saukin kai ko da kuwa ba kyakkyawa bane, amma kuma bana son mummuna (Alllah na tuba), Ina son namiji mai tsafta, bana son kazami. Irin Auren da nake buri ayi min shi ne wanda za mu sha shagali irin na zamani bana son auren zamanin daya shude na fi son na dai-dai zamani na ba wai karya za a yi a bikin ba amma dai a bawa bikin hakkinsa yadda ya kamata. Irin zaman auren da nake son yi da mijina in Allah ya nufa, ina son mu yi zaman cikin soyayya kamar dai soyayya ta saurayi da budurwa bana son zaman da za ki ga namiji na hantarar mace bana son irinsa.
Daga Arfa Ibrahim Jihar Kebbi

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
  • Sulaiman
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • Sulaiman
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • Sulaiman
    Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Bukatar Koya Wa Yara Zama Lafiya Da Kowa

Bukatar Koya Wa Yara Zama Lafiya Da Kowa

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.