Iyayen ɗaliban da aka sace a makarantar sakandaren gwamnati da ke Lassa, a ƙaramar hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno, sun bayyana cewa suna cikin tsananin damuwa tun bayan harin da aka kai makarantar.
Sun ce tun daga lokacin da suka ji labarin harin, ba su san inda ‘ya’yansu suke ba, kuma babu cikakken bayani kan adadin ɗaliban da aka sace ko halin da suke ciki.
Wani mazaunin Lassa ya shaida wa BBC Hausa cewa bayan ya ji ƙarar harbe-harbe, ya garzaya makarantar amma ya tarar kowa na gudu domin tsira d ransa.
Ya ce duk da cewa ‘ya’yansa sun tsira, har yanzu iyaye da dama ba su san inda ‘ya’yansu suke ba.
Rahotanni sun ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 9 na safiyar ranar Litinin, lokacin da ɗalibai ke tsaka da zana jarabawar NECO.
Ana zargin mayaƙan ISWAP ne suka shiga makarantar, suka yi ta harbe-harbe, sannan suka sace wasu ɗalibai da wasu mata masu sayar da abinci kafin su tsere zuwa cikin daji.
Kakakin rundunar ‘yansandan Borno, DSP Nahum Daso, ya tabbatar da faruwar harin.
Ya ce jami’an tsaro sun yi artabu da maharan, kuma suna ci gaba da farautarsu a cikin daji.
Har yanzu ba a tantance adadin mutanen da aka sace ba, yayin da ake ci gaba da bincike da aikin ceto waɗanda lamarin ya shafa.
Wannan hari ya sake tayar da hankalin al’ummar Borno, musamman saboda irin hare-haren da ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP ke ci gaba da kai wa makarantu da al’ummomin yankin.














