Wani rikici ya barke a zauren Majalisar Wakilai a ranar Laraba yayin da ‘yan Majalisar suka samu rashin jituwa kan kwamitin da ya kamata ya yi wa Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, CBN Olayemi Cardoso, tambayoyi kan zargin rashin tura fiye da Naira Tiriliyan 16 daga cikin kudaden shiga na gwamnati.
Hayaniyar ta biyo bayan amincewa da kudirin da dan majalisar Osun, Bamidele Salam ya dauki nauyi kan batun binciken zargin karkatar da kudaden shiga fiye da Naira Tiriliyan 16 daga Babban Bankin Nijeriya.
- ‘Yan Majalisa Sun Jaddada Ƙudirin Samar Da Shirye-shiryen Tallafawa Matasa
- An Kafa Kungiyar Abokai Ta Tafiyar Da Harkokin Duniya A Hedkwatar MDD
Salam ya bukaci Majalisar da ta gayyaci gwamnan CBN ya bayar da bayani tare da gabatar da “matakai masu dacewa” don biyan dukkan basussukan da ake bin Gwamnatin Tarayya nan take.
Dan majalisar Kano, Ghali Tijani daga baya ya nemi a yi kwaskwarima kan kudirin da ke nuna cewa za a kafa kwamitin wucin gadi don gudanar da binciken, kudirin kuma da Mark Esset na Akwa Ibom ya goyi baya.
Amma kudirin ya yi karo da ra’ayin wasu musamman dan majalisa Ahmed Jaha (APC, Borno), wanda ya ce, bai dace a ɗauke irin wannan binciken daga kwamitin da ke kula da binciken zargin almundahana ba zuwa wani kwamitin wucin gadi.














