ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Tsige Ni Aka Yi Ba, Ni Na Yi Murabus Da Kaina – Baba Impossible 

by Sadiq
4 years ago
Baba Impossible

Tsohon Kwamishinan Harkokin Addinai na Jihar Kano, Dakta Muhammad Tahar Adamu, ya ce shi da kansa ya yi murabus ba tsige shi aka yi ba.

Idan dai za a iya tunawa dai, kwamishinan yada labaran Jihar Kano, Malam Muhammad Garba ne, ya fitar da sanarwa a ranar Asabar, inda ya bayyana korar Baba Impossible a matsayin kwamishinan harkokin Addinai.

  • Abubuwan Da Suka Bambanta Harkar Fim Ta Da, Da Yanzu – Hajiya Zulaihatu
  • Sabuwar Shekara: Sanwo-Olu Ya Yi Wa Fursunoni 104 Afuwa

A wata hira da ya yi da gidan rediyon Freedom a ranar Asabar, Baba Impossible, ya bayyana mamakinsa kan labarin korarsa da gwamnatin jihar ta fitar, inda ya bayyana cewa shi da kansa ya mika takardar murabus dinsa a ranar Juma’a, 30 ga watan Disamba, 2022 ga sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji.

ADVERTISEMENT

Tsohon kwamishinan, ya ce ya yi mamakin jin a kafafen yada labarai cewa korarsa aka yi, wanda karya hakan.

Ya ce murabus din nasa ya samo asali ne bisa wasu dalilai na kashin kansa.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Baba Impossible ya ce gwamnatin jihar ta ci gaba da yin karya game da shi, amma ya ce hakan zai tilasta masa ya mayar da martani.

Sai dai a sanarwar da kwamishinan yada labaran jihar ya fitar, ‘’Korar kwamishinan harkokin Addinai na nan daram.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Korar da aka yi wa kwamishinan kuma dan majalisar zartarwa ta jihar ya biyo bayan halin rashin da’a ne a matsayinsa na ma’aikacin gwamnati mai rike da mukami, da kuma kalamai marasa kan gado.”

Malam Garba ya yi nuni da cewa, an kuma same shi yana gudanar da al’amuran ofishinsa ne a matsayin wajen sana’a, har ma yana rage ranakun aiki ga ma’aikatan ma’aikatarsa, inda ya kebe ranakun Laraba da Juma’a.

Kwamishinan ya kara da cewa baya ga gudanar da aiki ba tare da tuntubar gwamnati ba, Baba Impossible baya biyayya ga gwamnati.

Ya bayyana cewa gwamnan jihar ya aike da sunan Dakta Nazifi Ishaq Bichi na Jami’ar Bayero Kano zuwa majalisar dokokin jihar domin maye gurbinsa.

Gwamnan ya yi wa kwamishinan da aka kora fatan alheri a rayuwarsa ta gaba.

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Xinjiang Ta Soki Matsayar Amurka Ta Sanya Wani Kamfanin Fasaha Cikin Jerin Kamfanonin Da Ta Kakabawa Takunkumi

Xinjiang Ta Soki Matsayar Amurka Ta Sanya Wani Kamfanin Fasaha Cikin Jerin Kamfanonin Da Ta Kakabawa Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.