ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Tsige Ni Aka Yi Ba, Ni Na Yi Murabus Da Kaina – Baba Impossible 

by Sadiq
4 years ago
Baba Impossible

Tsohon Kwamishinan Harkokin Addinai na Jihar Kano, Dakta Muhammad Tahar Adamu, ya ce shi da kansa ya yi murabus ba tsige shi aka yi ba.

Idan dai za a iya tunawa dai, kwamishinan yada labaran Jihar Kano, Malam Muhammad Garba ne, ya fitar da sanarwa a ranar Asabar, inda ya bayyana korar Baba Impossible a matsayin kwamishinan harkokin Addinai.

  • Abubuwan Da Suka Bambanta Harkar Fim Ta Da, Da Yanzu – Hajiya Zulaihatu
  • Sabuwar Shekara: Sanwo-Olu Ya Yi Wa Fursunoni 104 Afuwa

A wata hira da ya yi da gidan rediyon Freedom a ranar Asabar, Baba Impossible, ya bayyana mamakinsa kan labarin korarsa da gwamnatin jihar ta fitar, inda ya bayyana cewa shi da kansa ya mika takardar murabus dinsa a ranar Juma’a, 30 ga watan Disamba, 2022 ga sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji.

ADVERTISEMENT

Tsohon kwamishinan, ya ce ya yi mamakin jin a kafafen yada labarai cewa korarsa aka yi, wanda karya hakan.

Ya ce murabus din nasa ya samo asali ne bisa wasu dalilai na kashin kansa.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Baba Impossible ya ce gwamnatin jihar ta ci gaba da yin karya game da shi, amma ya ce hakan zai tilasta masa ya mayar da martani.

Sai dai a sanarwar da kwamishinan yada labaran jihar ya fitar, ‘’Korar kwamishinan harkokin Addinai na nan daram.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Korar da aka yi wa kwamishinan kuma dan majalisar zartarwa ta jihar ya biyo bayan halin rashin da’a ne a matsayinsa na ma’aikacin gwamnati mai rike da mukami, da kuma kalamai marasa kan gado.”

Malam Garba ya yi nuni da cewa, an kuma same shi yana gudanar da al’amuran ofishinsa ne a matsayin wajen sana’a, har ma yana rage ranakun aiki ga ma’aikatan ma’aikatarsa, inda ya kebe ranakun Laraba da Juma’a.

Kwamishinan ya kara da cewa baya ga gudanar da aiki ba tare da tuntubar gwamnati ba, Baba Impossible baya biyayya ga gwamnati.

Ya bayyana cewa gwamnan jihar ya aike da sunan Dakta Nazifi Ishaq Bichi na Jami’ar Bayero Kano zuwa majalisar dokokin jihar domin maye gurbinsa.

Gwamnan ya yi wa kwamishinan da aka kora fatan alheri a rayuwarsa ta gaba.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Xinjiang Ta Soki Matsayar Amurka Ta Sanya Wani Kamfanin Fasaha Cikin Jerin Kamfanonin Da Ta Kakabawa Takunkumi

Xinjiang Ta Soki Matsayar Amurka Ta Sanya Wani Kamfanin Fasaha Cikin Jerin Kamfanonin Da Ta Kakabawa Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.