ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Wacce Ta Yi Sa’a A Masana’antar Fim Irina – Hajiya Sadiya Musa

by Rabi'at Sidi Bala
4 years ago
Sadiya Musa

A ci gaban tattaunawar da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA ta yi da fitacciyar Jarumar fina-finan Hausa ta Kannywood, kuma me taka rawa a cikin shirun Dadin Kowa wato HAJIYA SADIYA LAWAN MUSA wadda aka fi sani da SABUWAR MALAM AYUBA. Ta bayyana irin sa’ar da ta yi a masana’antar fim wadda take ganin babu kamarta. Ko me ya sa ta fadi hakan? Ga dai ci gaban tattaunawar kamar haka:

Bayan harkar fim da kike a yanzu, shin kina wata sana’ar ne?
Toh! Alhamdulillahi ina sana’o’i ma ba sana’a daya ba, tunda ni tun asali ba mace ba ce da take zama haka, ban saba zama haka ba, tun kan ma na fara fim ina sana’o’ina, in ta kama hakk dai harkoki ma kala-kala, kin san harkar mu na Mata, baya wuce kayayyaki na kwari, sannan kuma duk abin da yakama duk abubuwan da Mata suke bukata haka dai za ka dauko ka rinka siyarwa ana siya. Wasu lokutan ma har abin da za a ci ma ina sarrafawa, su abincin sayarwa haka dai a gida ko wani abu na sarrafawa wani zubin na bayar a fitar mun da shi, duk dai ina yi. Amma yanzu abin da ya fi karfi a sana’a ta shi ne sabulu, ina hada sabulun wanka Molato shi nake yi yanzu, ina hada sabulu da Mai, Alhamdulillahi kuma ya karbu har Nija ake kai mun kayana, daga can ma ana nema, don sun karbu sosai a can.

Mu dan koma baya kadan cikin shirin Dadin Kowa wanda ya fito a kanin Raliya da wanda ya fito a matsayin danki wato Dan Asabe, wasu na ta jita jitan cewa yaranki ne, me za ki ce akan hakan?
Ga baki dayansu dai ba wanda na haifa a cikinsu, duk aiku be ya hadani da su, shi wannan dan gidan Malam Barau kanin Raliya wannan katon nan, duk aikin ne ya hada ni da shi, shi ma kuma Dan Asabe mutumin Adamawa ne, aiki ne ya hada ni da shi, amma mutane da yawa suna tambayata ni kaina suna cewa ko ni na haife shi, tun da an ga yanayi kamar shi ma yana da hasken fata, ana tunanin kamar ko dana ne, duk aiki ne ya hada ni da su.

ADVERTISEMENT

Wa kika fi so a hadaki da shi ko ita a matsayin ‘yar ki ko danki?
Ai ni ba zan iya cewa ga wanda na fi so a hadani da shi ba, na yi ‘ya’yan da yawa, kin ga a haka ma a wasu fina-finan ma Daushe kan shi ya fito a dana, su me sana’ar nan duk sun fito a ‘ya’yana, Matan kuma na taba yin ‘ya da Hadiza Gabon, na yi da Fati Washa, su Hafsat Barauniya, duk yawanci duk sun fito a ‘ya’yana, kin ga kuwa ni kowa ma, duk wanda dai ya dace a hadaka a fim, kawai shikkenan sai ka ja rol, ba matsala.

Ko akwai wanda ya taba ko ta taba bata miki rai cikin masana’antar?
Wallahi ba kowa, ni dai ina ganin ma a cikin masana’antar ba wanda ya yi sa a dai Allah na tuba irina, tun da ni dai kowa dai wallahi muna zaman lafiya da su ni ban san dalilin hakan ba, da manya da yara da Maza da Mata ni dai in dai na fita aiki ko muka hadu a wajen wata sabga na harkar ‘yan indostiri za ki ga kowa faran faran muke da shi, ban taba fada da kowa ba, shiyasa ko a cikin kannywood din ma, ina ji da kunne na ana yabona, ana cewa ina da mutunci, mutane suna taka tsam-tsam da shiga harka ta, saboda sun ganni ba ni da hayaniya, ba ni da yawan magana, indai na je waje kawai zan zauna nayi shuru, abin da ya kaini shi zan yi in an gama in tashi na tafi gida, kuma ban yaho, bana bin kawaye, ba ni da wasu kawaye na harkoki haka daban-daban, ni dai buri na in an kirani aiki da na zo na yi alla-alla nake na yi maza na koma gida wajen ‘ya’yana, wallahi haka nake a indostiri.

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Wanne abu ne ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin haka wanda ba za ki taba mantawa da shi ba?
Babban abin da ya taba faruwa da ni na farin ciki ta dalilin harkar fim din nan, lokacin Nes lebil, lokacin da Shugaban Kasa Buhari za a yi wancen zaben da suka hau, lokacin an yi salaktin da ni a ciki, wanda za su je Bila, a je kamfen din Buhari muka je kuma mun samu kudi ba laifi, an ba mu makudan kudi a lokacin gaskiya shi ne na yi farin ciki sosai har kasa bacci na yi.

Me ya fi saurin saka ki farin ciki, me kuma ya fi saurin bata miki rai?
Abin da ya fi saurin sakani farin ciki shi ne na ji ni cikin kudi, wanda ya fi bata mun kuma shi ne saba alkawari.

A gaba daya fina-finan da kika yi wanne fim kika fi so wanda ya zama bakandamiyarki?
Shin din dana fi so shi ne fim din Juda.

Takaitaccen fim ne ko me dogon zango ne (series film)?
Takaitaccen film ne na RK studio

Wanne irin abinci da abin sha kika fi so?
Na fi son Wake da Shinkafa da Manja da Yaji da Salad. Abin sha kuma Zobo.

Wanne irin kaya kika fi son sakawa?
Na fi son Doguwar riga.

Wacce shawara za ki bawa masu kokarin shiga harkar fim da ma na ciki baki daya?
Ina so na ba da shawara ga wadanda suke cikin wannan harkar da da kuma wadanda suke kokarin shigowa cikin wannan harka tafim, akan in za su shigo ciki su dauke ta a matsayin sana’a kumk su riketa da zuciya daya, sannan kuma su ruke gaskiya a cikinta, shawarata kenan.

Ko akwai wani kira da za ki yi ga gwamnati game da cigaban masana’antar Kannywood?
Ina kira ga Gwamnati ta jiha da ta tarayya akan ta tsaya ta dubi harkar nan ta fim ba kananan mutane bane suke cin abinci a cikin wannan harka, yara Maza da Mata da iyaye magidanta, ba karamin ci gaba suke samu na taimako a cikin wannan harkar ba, masana’anta ce babba, wadda daruruwan mutane suke cin abinci a cikinta, ya kamata a ce gwamnati ta zo ta tsaya ta duba harkar nan, ta tallafa ta taimaka, saboda a cikinmu ma haka dai akwai iyaye gajiyayyu suna da ‘ya’ya da yawa da Mata, amma kuma sai ka gani fim din ma ba ruke su yake ba, tun da wani lokacin sai aiki ya ya samu ai sannan za a biya mutum, ba kamar aikin gwamnati ba ne da duk wata ko kayi ko baka yi ba za a baka kudinka, toh ya kamata su rinka shigowa ana tattaimakawa da yaran da manyan gaba daya.

A ciki kuma akwai wanda suke bukatar Aure ba su da kudin da za su yi, toh kin ga da ace gwamnati za ta rinka shiga cikin harkar a kungiyance za a samu a rinka solbin din irin wannan matsalolin, saboda a haka ma akwai yara da yawa Maza da suke so su yi aure ba su da karfin da za su yi, akwaiMata ma da suna zaune suna so su yi auren, ko zawarawa ko ‘Yan Mata, amma iyayensu ba su da karfin da za su taimaka musu na kayan daki, da kuma abin da za su dan samu su zauna gidan miji na sana’a, shiyasa za ki ga wani lokacin abin yake juyawa ya koma wata sigar daban.

Me za ki ce ga masoyanki?
Toh masoyana gaba daya ina yi musu fatan alkhairi, Allah ya bar zumunci da kauna.

Me za ki ce da wannan shafi na Rumbun Nishadi da kuma ita kanta Jaridar LEADERSHIP Hausa?
Ina yi wa wannan shafi na Rumbun Nishadi da kuma Jaridar LEADERSHIP Hausa, fatan alkhairi, ina mika godiya ta sosai a gare su, sannan kuma ina fatan Allah ya kara daukaka su.

Ko kina da wadanda za ki gaisar?
Ina gaishe da al’ummar musulmi gaba daya na fadin duniyar nan, kuma ina yi musu fatan alkhairi.

Muna godiya ki huta lafiya
Ni ma na gode

Sadiya Musa
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Jam'iyyar LP Ta Gargadi Shettima Kan Kalaman Batanci Da Yake Yi Kan Obi

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.