Mai magana da yawun babban yankin kasar Sin na ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Sin, Zhu Fenglian, ta sake nanata kudurin babban yankin wajen samar da zaman lafiya a sassan mashigin tekun Taiwan.
Mai magana da yawun ta bayyana hakan ne a yau Laraba lokacin da take amsa tambaya kan ziyarar da tawagar jam’iyyar Kuomintang ta kasar Sin (KMT) karkashin jagorancin shugabarta Cheng Li-wun ta kawo babban yankin kasar Sin.
Zhu ta ce, “A shirye muke, bisa la’akari da tushen siyasa mu tabbatar da yarjejeniyar 1992 da aka cimma da kuma adawa da batun ‘yancin kan Taiwan, don yin aiki tare da jam’iyyun siyasa, da kungiyoyi da daidaikun jama’a a Taiwan, ciki har da KMT, domin karfafa dangantakar da ke tsakanin mashigin ruwan biyu cikin lumana.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post