Wani mai magana da yawun babban yankin kasar Sin ya jaddada cewa bin ka’idar kasar Sin daya tak da kasashen duniya ke yi, wani lamari ne da ba za a iya kalubalanta ko kuma girgizawa ba.
Mai magana da yawun na ofishin kula da harkokin yankin Taiwan, na majalisar gudanarwar kasar Sin, Chen Binhua, ya yi wannan bayani ne jiya Litinin yayin da yake amsa tambaya daga manema labarai game da matakin da Babban Zauren Kiwon Lafiya na Duniya (WHA) na 79 ya dauka a jiyan, na kin shigar da shawarar da wasu kasashe suka gabatar kan shigar da Taiwan zauren a matsayin mai kallo, cikin ajandar taron zauren.
Ya yi nuni da cewa wannan ita ce shekara ta 10 a jere da zauren WHA ke kin amincewa da shawarwarin jeka-na-yi-ka masu alaka da Taiwan, inda Chen ya ce matakin ya sake nuna cewa tsayawa kan ka’idar Sin daya tak a duniya ita ce matsayar kasashen duniya.
Kazalika, a cewar mai magana da yawun, hakan ya kuma nuna cewa kokarin da mahukuntan jam’iyyar DPP suka yi na wai “samun nasara” game da shigar Taiwan zauren WHA ta hanyoyin kumbiya-kumbiya ya gaza cimma gaci.
Jami’in ya kuma yi nuni da cewa yankin Taiwan mallakin kasar Sin ne, kuma ’yan Taiwan ’yan uwa ne na babban yankin Sin. Duk da cewa Taiwan ba ta samu shiga zauren WHA ba, babban yankin Sin ya yi kyakkyawan tsari kan yadda yankin na Taiwan zai iya shiga a dama da shi a cikin harkokin kiwon lafiya na duniya a karkashin ka’idar Sin daya tak a duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post