Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya yi jawabi a jiya Litinin a yayin babban taron MDD na tunawa da “ranar kasa da kasa ta yaki da ra’ayin tsoron Musulunci”, inda ya jaddada cewa ya kamata kasashe su yi watsi da wannan ra’ayi na tsoron Musulunci, su nuna adawa da tsattsauran ra’ayi, da dakatar da tayar da rikici tsakanin mabambantan al’adu, kana su kauracewa yada kiyayya da rashin hakuri dangane da addini ko imani, kuma su yada al’adun zaman lafiya, da gina al’ummar bai daya ta kowa da kowa.
Sun Lei ya jaddada cewa, a halin yanzu, yakin da aka tayar a Gabas ta Tsakiya na ci gaba da wakana, kuma yana haifar da karuwar nuna bambanci, kyama, da tashin hankali, da kiyayya da nuna karfin tuwo ga Musulmai, wanda hakan ke kara dagula tsaro a yanki da duniya baki daya.
Jami’in ya ce, bangaren Sin yana adawa da alakanta ta’addanci da wata kasa, kabila ko addini. Kazalika, bangaren Sin zai ci gaba da kasancewa tare da kasashen Musulmi, don karfafa musayar wayewar kan Bil-Adam, da kuma kokarin samun ci gaba da wadata tare. (Amina Xu)















Discussion about this post