• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Taj Zai Kaddamar Da Manhajar Mu’amalar Banki Ta Salula

by Leadership Hausa
7 months ago
in Labaran Kasuwanci
0
Bankin Taj Zai Kaddamar Da Manhajar Mu’amalar Banki Ta Salula
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarinsa na saukaka wa kwastamominsa hada-hada da mu’amalar banki a duk inda suke, Bankin Taj da aka fi sani da ‘TajBank’ zai kaddamar da manhajar mu’amalar banki ta kashin kansa ba da jimawa ba.

Manhajar dai za ta kara kawo wa bankin kwastamomi da kara bunkasa ayyukansa a fadin Nijeriya.

  • Malam Ina So A Taimaka Mun Da Maganin Damuwa Da Bakin Ciki?
  • Jami’an Kashe Gobara Sun Ceto Mutum 91 Da Dukiyar Da Ta Kai Kusan Naira Miliyan 25 A Kano

Manajan Daraktan Bankin na Taj, Alhaji Hamid Joda ya bayyana haka yayin da mahukuntan Kamfanin Media Trust suka ziyarce shi a Abuja.

A ta bakinsa, “Muna shirin kaddamar da Bankinmu mai amfani da fasahar sadarwar zamani irinsa na farko a duk fadin Nijeriya kuma tsarin banki ne da wasu matasa ‘yan Nijeriya suka samar a nan cikin gida.

Yana kunshe da abubuwa daban-daban da zai iya gogayya da kafada da kafada da sauran ire-irensa na kasashen duniya.

Labarai Masu Nasaba

Karancin Kudi: Mun Yi Asarar Kwai Na Biliyan 30 -Masu Kiwo

Kamfanin Siminti Na Dangote Ya Samu Gaggarumar Riba Da Bunkasa A 2022

Muna sa rai mu kaddamar da shi ga jama’a cikin watan Satumba ko Oktobar nan mai zuwa, kasancewar muna jiran kammala wasu sharudda da samun amincewa.

Bankin na zamani an tsara shi ne musamman domin shigo da matasa cikin harkar banki kuma muna bukatar ‘yan jarida su yada labarinsa”.

Alhaji Joda ya kara da cewa bankin na Taj ya samu gagarumar nasara a kasuwar Nijeriya duk da kalubalen da aka fuskanta na annobar cutar Korona.

“2019 ta kasance shekarar da aka dan sha wuya saboda kalubalen annobar Korona.

Dama tun a farkon shekarar an sha wuya amma Alhamdu Lillah, mun samu nasarar magance kalubalen da aka fuskanta har aka samu riba cikin wata takwas da kafuwa.

Baya ga haka, mun samu nasarar biyan kudaden gudanar da ayyukanmu a shekarar farko ta fara kasuwanci kuma muka ci riba duk dai a shekarar ta farko wanda ba a saba ganin hakan ba a bangaren hada-hadar bankuna.”

Wakazalika ya kara da cewa bankin ya yi nasarar kara yawan jarin hada-hadarsa daga Naira Biliyan 50 zuwa Naira Biliyan 140.

Haka nan ya ce ba da jimawa ba TajBank zai kaddamar da Shirin Lamuni na SUKUK na Naira Biliyan 100.

Tags: Bankin TajKasuwanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matakai Shida Na Samun Nasara Ga ‘Yan Kasuwa

Next Post

Yadda Bikin Bai Wa Sarkin Bwari Sanda Ya Gudana A Abuja

Related

Karancin Kudi: Mun Yi Asarar Kwai Na Biliyan 30 -Masu Kiwo
Labaran Kasuwanci

Karancin Kudi: Mun Yi Asarar Kwai Na Biliyan 30 -Masu Kiwo

1 week ago
Kamfanin Siminti Na Dangote Ya Samu Gaggarumar Riba Da Bunkasa A 2022
Labaran Kasuwanci

Kamfanin Siminti Na Dangote Ya Samu Gaggarumar Riba Da Bunkasa A 2022

2 weeks ago
Madubin Sauyin Kudi Daga Wasu Kasashen Duniya Masu Tasowa
Labaran Kasuwanci

Madubin Sauyin Kudi Daga Wasu Kasashen Duniya Masu Tasowa

4 weeks ago
Kamata Ya Yi A Daure Duk Dan Kasuwar Da Ke Shigo Da Tufafi Nijeriya Daga Kasar Waje —Dangote
Labaran Kasuwanci

Kamata Ya Yi A Daure Duk Dan Kasuwar Da Ke Shigo Da Tufafi Nijeriya Daga Kasar Waje —Dangote

2 months ago
Rigima Ta Ƙare, CBN Ya Ƙara Adadin Kuɗin Da Za A Iya Cirewa A Mako
Labaran Kasuwanci

Rigima Ta Ƙare, CBN Ya Ƙara Adadin Kuɗin Da Za A Iya Cirewa A Mako

3 months ago
Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet
Labaran Kasuwanci

Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

4 months ago
Next Post
Yadda Bikin Bai Wa Sarkin Bwari Sanda Ya Gudana A Abuja

Yadda Bikin Bai Wa Sarkin Bwari Sanda Ya Gudana A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.