Masu ruwa da tsaki a ɓangaren harkokin jiragen ruwa da kasuwancin kan iyaka sun yi zargin cewa haramcin da gwamnatin tarayya ta sanya kan shigo da motoci ta land borders ya jawo wa Nijeriya asarar biliyoyin Naira na kuɗaɗen shiga a duk shekara, tare da ƙarfafa ayyukan fasa ƙwauri ta hanyoyin da ba a amince da su ba.
Da yake magana kan tasirin wannan manufa, shugaban kuma babban jami’in gudanarwa na kamfanin Only God is Wise Nigeria Limited, wanda ke gudanar da bonded terminal a iyakar Seme Border, Alhaji Adetona Mubashiru, ya buƙaci Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Adewale Adeniyi, da ya tura batun sake duba wannan dokar da aka shafe shekaru tara ana aiwatarwa.
Gwamnatin Tarayya ta hannun Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta sanar a watan Disambar 2016 cewa ta haramta shigo da sabbin motoci da tsofaffi ta kan iyakokin ƙasa, inda ta umarci cewa duk motocin da za a shigo da su su riƙa zuwa ta tashoshin jiragen ruwa daga ranar 1 ga Janairun 2017.
Mubashiru ya bayyana cewa manufar ta gaza cimma burinta na daƙile fasa ƙwauri da inganta sa ido kan motocin da ake shigowa da su. A maimakon haka, ya ce ta karkatar da halalcin kasuwanci zuwa ƙasashe maƙwabta da kuma hanyoyin kan iyaka da ba a amince da su ba.
A cewarsa, dokar ta tilasta masu shigo da kaya amfani da tashoshin jiragen ruwa masu cunkoso, yayin da wasu da dama suka koma amfani da hanyoyin jeji ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ya sa aikin jami’an Kwastam ya fi wahala tare da hana Nijeriya samun manyan kuɗaɗen shiga daga haraji.
Ya ce: “Maimakon dakatar da shigo da haramtattun kaya, dokar ta mayar da kasuwancin zuwa ɗaruruwan hanyoyin da ba a amince da su ba. Hukumar Kwastam ta fuskanci ƙalubale sosai wajen sa ido kan waɗannan hanyoyi yayin da gwamnati ke ci gaba da rasa kuɗaɗen shiga masu yawa duk shekara.”
Ya ƙara da cewa ƙasashe maƙwabta sun amfana sosai daga wannan manufa, domin masu shigo da kaya da dama sun karkatar da kayansu zuwa tashoshin jiragen ruwa da ke wajen Nijeriya, musamman a Benin Republic, inda ake ci gaba da jigilar motocin da aka nufa zuwa Nijeriya.
Mubashiru ya tunatar da cewa tsohon Kwanturola Janar na Kwastam, Hameed Ali, ya kare manufar a matsayin matakin da zai taimaka wajen yaƙi da takardun bogi da kuma shigo da motoci ba bisa ƙa’ida ba ta kan iyaka.
Sai dai Mubashiru ya dage cewa tun kafin dokar ta fara aiki, akwai yarjejeniya tsakanin Nijeriya da Benin Republic kan sa ido da jigilar motocin transit ta iyakar Seme ƙarƙashin kulawar jami’an Kwastam.
Ya bayyana cewa motocin da ke zuwa daga tashar jirgin ruwa ta Cotonou ana raka su zuwa iyaka sannan a miƙa su ga jami’an Kwastam na Nijeriya domin tantancewa, yana mai cewa matsalolin aiki kamar rashin isasshen filin ajiye motoci an magance su yanzu.
“Yanzu abubuwa sun canza. Iyakar Seme na da wuraren da za su iya ɗaukar motoci sama da 1,000 cikin sauƙi, wanda hakan zai sa tsarin ya zama mai tsari da gaskiya,” in ji shi.
Mubashiru ya kuma ce dokar ta shafi dubban ƴan Nijeriya da rayuwarsu ta dogara da harkar shigo da motoci, ciki har da dillalan kaya, direbobi, bakanikai, masu gyaran motoci da masu fenti da sauran masu sana’o’i a yankunan kan iyaka.
Ya roƙi shugabannin Kwastam na yanzu da su ba gwamnatin tarayya shawarar sake nazarin dokar bisa tsarin sauƙaƙa kasuwanci na duniya da kuma buƙatun masu ruwa da tsaki domin samar da tsarin shigo da kaya mai anfani ga tattalin arziki da gaskiya.
Mubashiru ya bayyana ƙwarin gwiwarsa cewa sake buɗe kan iyakoki domin shigo da motoci zai ƙara halalcin kasuwanci, samar da ayyukan yi da kuma bunƙasa kuɗaɗen shiga na gwamnati.














Discussion about this post