ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

by Shuaibu Shuaibu
3 weeks ago
Gwamna

Bayan samun goyon bayan Gwamnan Jihar Gombe, an amince da Jamilu Isyaku Gwamna, a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a zaben fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a watan da ya gabata.

Yanzu a babban zaben 2027 Gwamna zai fafata da Bala Tinka na jam’iyyar ADC, da kuma Isa Pantami na jam’iyyar PDP, wanda dukkansu -Tinka da Pantami, sun koma sabbin jam’iyyunsu ne bayan sun gaza samun tikitin takara a APC.

Yayin da yake sanar da Gwamna a matsayin dan takarar APC, Gwamna Inuwa Yahaya, ya bayyana shi a matsayin gogaggen dan siyasa kuma kwararren ma’aikacin gwamnati da ke da karbuwa a tsakanin al’umma, wanda a cewarsa Gwamna yana da amana da kuma tasirin da zai tabbatar wa jam’iyyar nasara a zabe mai zuwa.

ADVERTISEMENT

Da yake nuna godiyarsa kan wannan amana, Jamilu Gwamna, ya yi alkawarin ci gaba da dora wa kan nasarorin da gwamnatin Jihar Gombe ta samu tare da daga martabar jihar zuwa wani sabon matsayi na ci gaba.

Samun tikitin jam’iyyar APC mai mulki wani muhimmin sauyi ne a tafiyar siyasar Gwamna, wanda tun a shekarar 2007 ya fara neman kujerar gwamnan jihar Gombe karkashin jam’iyyar ANPP.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

A lokacin yakin neman zabensa na 2007, Gwamna ya ziyarci shalkwatar Kamfanin LEADERSHIP Group, inda ya bayyana burinsa da hangen nesansa na ci gaban Jihar Gombe.

Shekaru kusan ashirin kenan yana jiran wannan dama inda samun tikitin jam’iyyar mai mulki, wanda bai taba samu a baya ba, ya kusantar da shi ga cikar burinsa na zama gwamna, abin da ma sunansa “Gwamna” ke nuni da shi.

A shekarar 2011, ya shaida yadda dan uwansa, Ibrahim Dankwambo, ya bar aikin gwamnati a matakin tarayya tare da samun tikitin PDP, wanda ya kai shi ga zama gwamnan jihar.

Bayan shekaru takwas, yanayin siyasa bai ba da damar wani dan uwa ya gaji wani a kujerar gwamna ba amma daga bisani, a shekarar 2022, bayan ya kasa samun tikitin PDP, Jamilu Gwamna ya fice daga jam’iyyar tare da mara wa wa’adin mulki na biyu na Gwamna Inuwa Yahaya baya.

A wancan lokaci ma, Gwamna ya soki PDP, yana mai cewa jam’iyyar ba ta shirya karbar mulki ba inda aka rawaito shi yana cewa; “A gare ni wannan mataki shawara ce ta kaina, tun da ban shirya yin ritaya daga siyasa ba, dole na nemi wata hanya, kuma wannan hanyar ita ce komawa APC.”

Duk da haka, ya jaddada cewa goyon bayan da ya bai wa Inuwa Yahaya, ba don wata bukata ta kansa ba ne, sai dai saboda ci gaban jihar da kuma imaninsa cewa gwamnan na gudanar da aiki mai kyau kuma zai iya yin fiye da haka.

Yanzu alamu na nuna cewa wannan amincewa da goyon bayan da ya bai wa Gwamna Inuwa Yahaya, sun fara haifar masa da da mai ido, domin gwamnan ya nuna masa irin wannan karamci ta hanyar mara masa baya domin samun tikitin takarar gwamna.

Gwamna
Shuaibu Shuaibu
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
Bakon Marubuci

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.