ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya

by Alhaji Adamu Rabiu and Sulaiman
4 weeks ago
Dimokuradiyya

Lokacin da matasan Najeriya za su hallara a zauren babban taron matasa na kasa, daga 7 zuwa 21 ga Yulin 2025 a birnin Abuja, tambaya guda daya ce za ta mamaye tattaunawar a karkashin jigo mai taken “Gudanar da Mulki Da Shiga Harkokin Siyasa”.

Ta yaya za mu dora siyasarmu a kan turba madaidaiciya, sannan kuma mu ceto dimokuradiyya daga hannun azzalumai a Nijeriya? A matsayina na mai gabatar da wannan kasidar tsarin manufofi zuwa kwamitin shirya taron, ban tsaya kan bayyana matsaloli kadai ba, na zo da cikakken shiri na ceto dimokuradiyyar wannan kasa.

Nijeriya na fama da mummunar matsalar rashin kyakkyawan fasilin siyasa, inda masu kudin haram ke karbe jam’iyyun siyasa, fagen siyasa ya zama cike da hadura da dungu, zabe ya koma yaudara, inda wanda ya ci zabe shi kadai ke cin moriyarta, ’yan gudun hijira sun rasa damar kada kuri’arsu, sannan hukumomin zabe na jihohi, sun zama karen farautar masu rike da madafun iko a jihohi, sannan suna yi wa gaskiya da rikon amana rikon sakainar-kashi.

ADVERTISEMENT

Wadannan matsaloli da wasu ma, na bukatar matasa su yi karatun ta-nutsu, su kuma  dauki matakin gaggawa; domin ceto Nijeriya daga hannun azzalumai, kana su kuma dora ta a kan turba madaidaiciya.

Matsalolin Da Muke Fuskanta:                    

LABARAI MASU NASABA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

Bayan shekar 22 da kubutar da Nijeriya daga mulkin soja, dimokuradiyya na ci gaba da fama da rauni mai tsanani. Alamun cutar sun bayyana ne a cinikin baragurbin wakilai (delegates), amfani da kudin kasa da aka wawure ta hanyar haram wajen gudanar da yakin neman zabe, makudan kudin da ake ware wa Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), karancin yawan masu kada kuri’a, sayen kuri’u a bainar jama’a, tashin hankali yayin zabe, da kuma yaduwar fargaba, musamman a tsakanin matasa, cin amana na ’yan siyasa, canja sheka da zababbu ke yi, da dai sauran makamantansu.                                      

Asalin matsalar ita ce, rashin shiga cikin gudanar da gwamnati a siyasance (edclusion) na masu gaskiya da rikon amana, matasa, mata, masu fama da nakasa, ‘yan gudun hijira da jam’iyyun da ke da karamin karfi, duk sun kasance a wajen filin.

Wannan ba kawai rashin adalci ba ne, har ma ya saba wa kundin tsarin mulki, kuma barazana ce ga zaman lafiya da ci gaban kasa. Idan ka duba, za ka fahimci cewa; dimokuradiyyarmu na hannun wasu tsirarun mutane da shugabannin jam’iyyu masu karfi, wadanda suka killace matasa da sauran ‘yan Nijeriya daga samun damar shiga siyasa ko a saurare su ko la’akari da tasu gudunmawar. Dimokuradiyyar cikin gida a jam’iyyu, abin dariya ne kawai, domin an mayar da zabe na cikin gida zuwa ciniki, wato ba ni kudi ga kuri’a. Inda a wani bangaren kuma, INEC na fuskantar kalubalen rashin ’yanci da rashin kwarin guiwar aiwatar da dokokinta.

Har ila yau, ‘yan gudun hijira da sauran al’umma masu rinjaye ana ci gaba da ware su daga zabe. Haka nan, hukumar zaben jihohi, musamman yadda aka gani a zaben kananan hukumomi a Kaduna da Bauchi, sun zama wani kwafi da ya ci mutuncin dimokuradiyya. Wannan ya saba wa sassa da dama na Kundin Tsarin Mulki na 1999 (Sashe 14(2)(a), 15(1), 40, 153(1)(f), 221, 318(1), da Jadawali na Bakwai), da Dokokin Kungiyar Tarayyar Afirka da kuma Majalisar Dinkin Duniya.  

Yadda Wannan Tsari Na Matasa Zai Taimaka Wajen Ceto Siyasarmu:

1-Yarjejeniya Ta kasa Don Siyasa Mai Inganci (National Charter for Inclusion): A samar da wata Yarjejeniya ta hadin gwiwa tsakanin Ma’aikatar Matasa ta Kasa, Kungiyar Gamayyan Jamíyyun Siyasa (IPAC), Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), Kungiyoyin Fararen Hula da Majalisar Matasa ta Nijeriya. Wannan yarjejeniya za ta kafa ka’idoji da dokokin da za su tilasta dimokuradiyya a cikin jam’iyyu, tabbatar da adalci wajen zabubbuka da kuma bai wa dukkannin jam’iyyun da suka shiga zabe damar ba da gudunmuwa wajen shugabanci a kowane mataki da kuma bai wa matasa, mata, ‘yan gudun hijira da kowa da kowa damar ’yancin tsayawa takara cikin adalci. 

2- Sauyi Mai Zurfi Ga Jam’iyyu da Tsarin Zabe: Ya zama wajibi jam’iyyu su bude kofa. A kafa dokar da za ta tilasta duk mai son tsayawa takara gabatar da “Tsarin Ayyuka” (Project Plans) kafin hawa kujera, sannan ya fitar da “Rahoton Karshe” (End-of-Term Reports), bayan barin gado ko da kuwa zai koma kuwa. A dakile kudin da ake nema marasa tushe daga masu neman takara, musamman na hukumomin zaben jihohi, (Misalin KAD-SIECOM). A tabbatar da cikakken amfani da Sashe na 7 na Kundin Tsarin Mulki da Dokar Zabe ta 2022.  

3- Runguman Dimokuradiyyar Dijital Hannu Biyu (Digital Democracy): A kafa “Cibiyar Dimokuradiyyar Dijital ta Kasa (NDDH)” da za ta sa ido, bayar da rahoto kai tsaye, sa ido kan kudin yakin neman zabe da tantance tsarin jam’iyyu. Za ta kuma ba da damar samun ilimin siyasa ta hanyar wasanni da fasahar zamani domin kara fahimta, rage rashin sha’awa daga matasa, da bunkasa ilimi da rikon amana.

4- Karfafa IPAC Youth da Shirye-shiryen Fadakarwa: A karfafa Bangaren Matasa na IPAC (IPAC Youth Directorate) daga matakin kasa har zuwa jihohi, ta hanyar samar da doka, kasafin kudi da kuma tsarin aiki. Sannan, a dora musu alhakin wayar da kan jama’a a fadin kasar nan, musamman a tsakanin wadanda aka ware daga siyasa.

Me Za Mu Samu Idan An Bi Wannan Hanya? Za mu samu dimokuradiyya mai inganci da kuma tsabta, inda matasa, mata, masu fama da nakasa (PWDs) da ‘yan gudun hijira (IDPs) za su samu bakin fada kuma a ji a cikin siyasa da shugabanci. Za a samu karancin tashin hankali a lokacin zabe, raguwar sayen kuri’a da ingantaccen ilimi da wayewa a tsakanin jama’a.  Za kuma a samu jam’iyyu masu gaskiya da amana da kuma shugabanci na kwarai da ci gaban kasarmu Nijeriya.

Matakan Aiwanar Da Wannan Tsari:

Mataki na 1: Rubuta NSPPC tare da dukkan masu ruwa da tsaki.

Mataki na 2: Kafa tsarin dubawa tsakanin INEC, IPAC da CSO.

Mataki na 3: Kaddamar da NDDH da kayan aikin ilmantarwa.

Mataki na 4: Gyaran Dokar Zabe, domin shigar da wadanan al‘amura da muka gabatar a sama da sauran bukatu.

Kafin Mu Kammala: Makomar dimokuradiyyar Nijeriya na cikin hadari. Ba za mu iya ci gaba da kallon halin da ake ciki ba na rashin adalci, cin amana, zangon kasa ga kasa da al’úmarta.

Yazama wajibi mu yi amfani da karfin matasa, domin ceto Nijeriya daga bakin kuraye. Kirkire-kirkire da bukatar rikon amana, su ne maganin cutar da dimokuradiyyarmu ke fama da ita.

Wannan tsari nawa na zuwa ne daga gwanancewa da aiki da IPAC, shirye-shiyen fitar da sakwanni ta ‘Bakondare Speaks’, wallafa rubuce-rubuce a manyan jaridu kamar su Premium Times, Daily Trust, Guardian, Punch, Banguard, Thisday , Leadership (A hausance da turanci)) da kuma shiga ayyukan siyasa masu tsafta da kuma alaka da kungiyoyi masu muhimmanci na siyasa.  

Yanzu ne lokacin sauyi! Muryar matasa ya kamata ta koma tsakiya wajen tsara manufofi da aiwatar da su. Yakamata dimokuradiyyar Nijeriya ta amfani kowa da kowa ba wasu ba kawai!

Kafin rahoton karshe na wannan taro ya isa ofishin Shugaban Kasa ranar 12 ga Agusta, 2025 (Ranar Matasa ta Duniya), ina kira da babbar murya da fatan alheri ga duk dan Nijeriya da kuma dukkan wakilai da su rungumi wannan tsari. Ina kuma kira ga ’yan majalisa da masu zartarwa da su aiwatar da shi, domin ci gaban Nijeriya da kuma amfanin masu zuwa nan gaba. Yanzu ne lokacin daukar mataki na hakika da Jarumta! Allah ya yi mana albarka, ameen.

Dimokuradiyya
Alhaji Adamu Rabiu
+ posts Bio
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    Rashin Tsaro A Nijeriya: Gazawar Masu Mulki Ce Da Cin Amanar Ƙasa
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
Dimokuradiyya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
obi
Bakon Marubuci

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

May 16, 2026
Dawowar Ayyukan ‘Yan Kunar Bakin Wake
Bakon Marubuci

Dawowar Ayyukan ‘Yan Kunar Bakin Wake

May 1, 2026
Next Post
Amfanin Man Kwakwa Guda 12

Amfanin Man Kwakwa Guda 12

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.