ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

by Shuaibu Shuaibu
45 seconds ago
Dangote

Attajirin da ya fi kowa arziki a Afirka, Aliko Dangote, kwanan nan ya halarci wata tattaunawa ta podcast mai suna ‘In Good Company’.

Tattaunawar ta fi mayar da hankali kan jarin da Dangote ke zubawa, amma yanayin tambayoyin da amsoshin da ya bayar, sai suka yi kama da irin wadanda mai neman aiki ke bayarwa.

Tabbas ba neman aiki yake yi ba. An kiyasta arzikin Dangote ya kai kusan dala biliyan 30, kuma a cikin tattaunawar ya bayyana shirinsa na zuba jarin fiye da dala biliyan 45 a nahiyar Afirka.

ADVERTISEMENT

Amma shirin ‘In Good Company’, babbar nasara ce ga Dangote saboda kasancewar shirin, ya fi mayar da hankali ne kan manyan ’yan kasuwa, shugabannin duniya da fitattun masu tunani.

Dangote ya burge mai gabatar da shirin, Nicolai Tangen, da kwarin gwiwarsa da kuma shirinsa na zuba makudan kudade a Afirka, ciki har da gina daya daga cikin manyan cibiyoyin masana’antu a nahiyar — matatar mai ta dala biliyan 20 mai karfin tace ganga 650,000 a rana.

LABARAI MASU NASABA

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

Dangote ya nuna kwarewarsa sosai yayin tattaunawar, inda ya yi magana kan ladabi a kasuwanci, muhimmancin hangen nesa da kuma fahimtar bukatun kasuwannin Afirka.

A cewarsa, daya daga cikin manyan bukatun nahiyar shi ne samar da siminti, wanda kasashen Afirka da dama ke fama da karancinsa. Ya ambaci Nijeriya, Zambia da Congo Brazzabille a matsayin kasashen da suke zaman jira har watanni uku kafin su samu siminti.

Da aka tambaye shi inda ya samo kudin gina matatar mai, Dangote ya bayyana bayanai fiye da yadda ya saba yi. Game da bambance-bambancen al’adun kamfanoni a Afirka da wahalar gudanar da kasuwanci, Dangote bai raina nahiyar ba.

Maimakon haka, ya fi mayar da hankali kan al’adun aiki a cikin kamfanoni daban-daban da kuma matakin horas da ma’aikata, wanda ya ce za su iya yin nasara a duk inda suka shiga a fadin duniya.

Dangote har ya ambaci makarantar horaswa da kamfaninsa ke gudanarwa domin zakakuran dalibai daga jami’o’in Nijeriya da sauran kasashen Afirka.

Nicolai Tangen, ba kawai mai gabatar da podcast ba ne; shi ne babban jami’in gudanarwa na ‘Norges Bank Inbestment Management’, wanda ke kula da Asusun Arzikin Kasa na Norway.

Asusun na Norway shi ne mafi girman asusun gwamnati na zuba jari a duniya, inda yake da kadarori da suka haura dala tiriliyan 2.

Yana da hannun jari a kamfanoni 7,200 a kasashe 70 na duniya.Tattaunawar podcast din da Dangote ya yi wani bangare ne na tattaunawa da hadin gwiwar asusun domin zuba jari a Dangote da kuma Afirka baki daya.

Dangote
Shuaibu Shuaibu
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
Bakon Marubuci

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

June 12, 2026
Dimokuradiyyar Nijeriya A Shekara 27:Ba Yabo Ba Fallasa

Dimokuradiyyar Nijeriya A Shekara 27:Ba Yabo Ba Fallasa

June 12, 2026
Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

June 12, 2026
Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

June 11, 2026
Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

June 11, 2026
Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

June 11, 2026
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda

June 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.