Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayyana cewa ya bai wa wasu yankuna a jihar damar yin sulhu da ’yan bindiga bayan mazauna yankunan sun roƙi a ba su damar neman zaman lafiya da kansu.
Da yake magana a wata hira da shirin Sunrise Daily, Radda ya ce al’ummomi da dama sun sha fama da hare-haren ’yan bindiga kuma suna ganin ba sa samun kariya daga jami’an tsaro.
A cewarsa, al’ummomin sun zo wajensa suna neman izinin tattaunawa da ’yan bindigar domin samun zaman lafiya da kuma komawa harkokinsu na yau da kullum.
Gwamnan ya ce ya amince su tattauna, amma ya jaddada cewa shi da kansa ba zai kasance cikin sulhu ko tattaunawa da ’yan bindiga ba.
Radda ya ƙara da cewa wasu daga cikin al’ummomin da suka cimma yarjejeniya da ’yan bindigar sun shafe sama da shekara guda ba tare da an kai musu hari ba.
Ya ce yanzu yawancin mazauna yankunan na iya zirga-zirga cikin kwanciyar hankali tare da komawa gonakinsu.
Sai dai gwamnan ya nanata cewa ba zai taɓa gayyatar ’yan bindiga su ajiye makamansu ko tattaunawa da su kai-tsaye ba.
Ya bayyana cewa shawarar yin sulhun ta fito ne daga al’ummomin da abin ya shafa, ba daga gwamnatinsa ba.















Discussion about this post