Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya buƙaci jam’iyyun adawa a Nijeriya su sake tunani kan shirin miƙa takarar shugaban ƙasa a 2027 ga yankin Kudu, yana mai cewa hakan na iya raunana damar kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓe mai zuwa.
A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Olusola Sanni, ya fitar ranar Litinin, Atiku ya bayyana cewa kiran da ake yi na bai wa Kudu tikitin shugaban ƙasa a jam’iyyun adawa na ɗauke da haɗarin siyasa kuma ba shi da cikakken dabarun cin zaɓe.
Ya ce duk da cewa jam’iyyar APC mai mulki na iya ci gaba da barin mulki a hannun ɗan Kudu domin kare shugaban ƙasa mai ci, bai kamata jam’iyyun adawa su ɗauki irin wannan matsayi ba tare da nazarin gaskiyar siyasa da ƙididdigar zaɓe ba.
“shirin siyasa ya kamata ya dogara da dabaru, da haɗin gwuiwa da lissafin nasara, ba wai son zuciya ko motsin rai ba,” in ji sanarwar. Atiku ya ƙara da cewa tarihin siyasar Nijeriya bai taɓa nuna inda ɗan takarar adawa daga yanki ɗaya ya kayar da shugaban ƙasa mai ci daga yankin nasa ba.
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya kuma yi zargin cewa wasu daga cikin masu goyon bayan tsarin karɓa-karɓar mulki sun yi watsi da shi a shekarar 2011 bayan rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Umaru Musa Yar’Adua, lokacin da suka mara wa Goodluck Jonathan baya domin ci gaba da mulki daga Kudu.
Sai dai Atiku ya amince cewa burin yankin Kudu maso Gabas na samar da shugaban ƙasa halastacce ne, amma ya gargadi jam’iyyun adawa da kada su rungumi tsarin da zai ƙara wa Shugaba Tinubu ƙarfin sake lashe zaɓe a 2027.















Discussion about this post