Tsohon gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ambaci Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano a hukumance.
Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin bikin rantsar da sabon Mataimakin Gwamnan Kano, Murtala Sule Garo, da aka gudanar a Fadar Gwamnatin Kano.
A lokacin jawabinsa, ya gaishe da Sarkin tare da kiran sa da cikakken matsayi na sarautarsa, abin da ya jawo tafi daga mahalarta taron.
Wannan ne karo na farko da Ganduje ya fito fili ya amince Sanusi a matsayin Sarkin Kano tun bayan saɓanin da ya shiga tsakaninsu, wanda ya kai ga tube shi daga sarauta a shekarar 2020 lokacin yana gwamna.
Lamarin na da matuƙar muhimmanci a siyasa da al’adun Kano, domin ya nuna alamun sauyin yanayi a dangantakar da ke tsakanin manyan jiga-jigan biyu bayan shekarun da aka kwashe ana takaddama.
A baya dai, an sauke Sanusi daga sarauta a 2020, kafin daga bisani gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta dawo da shi kan karagar mulki a shekarar 2024.
Wannan mataki na Ganduje na iya zama wata alama ta sassauta rikicin siyasa da na sarauta a Kano, musamman a wannan lokaci da siyasar jihar ke fuskantar sauye-sauye.















Discussion about this post