ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Rabiat Sidi Bala

Masarautar Shukra da ke kasar Ghana, daya ce daga cikin masarautun Hausawa masu dogon tarihi a kasar. A wannan tattaunawa ta musamman da Sarkin masarautar, wanda ya shafe shekaru 42 a kan karaga, ya bayyana abubuwa masu tarin yawa da tabbas masu karatu za ku so ku ji: Ga hirar kamar yadda wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA ta gudanar kamar haka:

 

Bari mu fara da takaitaccen tarihin mai martaba sarki

ADVERTISEMENT

Da farko dai sunana Alhaji Ibrahim Hamidu Dantani. An haife ni a wurin da ake kira Sabon Zango cikin Accra a kasar Ghana. Daga nan ne fatauci na iyayena ya taho damu zuwa garin Shukura. A wannan lokacin Shukura dokar daji ne sosai babu lantarki, babu ruwa na fanfo sai rijiya. To, haka nayi rayuwa tare da iyayena biyu da kanina mai suna Haruna Tsoho, da wasu jama’a kadan a cikin Shukura. Haka rayuwa ta cigaba, lokacin da na girma na auri mata ta ta farko mai suna Hadiza Ibrahim, muka haifi ‘ya’ya tara, a cikinsu mata bakwai da maza biyu. Daga baya na auri mata ta biyu mai suna Zainab Raibero, ita ta fito cikin wata kabila da ake kira Ga, a cikin wannan kasar ba musulmai bane, amma Allah ya ba ni iko na mayar da ita musulma kuma na aure ta. Kuma a wurinta Allah ya ba mu baiwar ‘ya’ya maza biyu. Haka al’amarin ya tafi har lokacin da sarauta ya zo kaina a shekarar 10th August 1983. Bayan wasu shekaru kadan da nadin sarauta iyayena suka koma ga Allah, sai kuma shekaru biyu da suka wuce a lokacin nan kuma na rasa matata ta biyu. A yanzu shekara arba’in da biyu nake akan kujerar sarauta sai mu ce Alhamdulillah.

 

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Zuwa yanzu sarakuna nawa aka yi a wannan masarauta ta Shukura?

A takaice dai sarakuna biyar aka yi a wannan masarauta ta Shukura. Na farko shi ne mai martaba sarki mai suna Atiya. Shekara uku ya yi a kan kujerar, sa’annan dan sa mai suna Haruna Atiya ya maye masa bayan rasuwar sa. Shekara biyu sarki Haruna yayi sarauta, ya koma ga Allah, sai mai martaba sarki Baba Mahmudu ya zauna a kan kujerar sarautar. Baba Mahmudu ya yi shekara daya shi ma ya koma ga Allah, sai sarauta ya koma ga hannun mai martaba Baba Zango. Bayan shekara uku Allah ya yi wa mai martaba Baba Zango rasuwa a lokacin ni ne Galadiman sa sai mutanen Shukura suka amince da cewa sarauta ta koma kaina. To yadda aka yi nake kan karagar mulki kenan har a yau.

 

Mai martaba sarki hakika mun samu labarin cewa, kusan ba a yi sarki da ya dade a kan karagar mulki kamar ka ba, shin mene ne sirrin dadewarka a sarauta?

To, farko dai sai mu ce Alhamdulillah, domin wani baiwa ne daga Allah ba iyawar mu ba ne. Ubangiji ne a cikin ikonsa ya ke aiwatar da abin da ya ga dama. Shi sirrin dadewa a kan karagar mulki daga Allah ne kawai.

 

Dole a cikin wannan tsahon tafiya da aka yi mai martaba sarki, akwai wasu abubuwa da aka fuskanta na kalubale, ko za ka iya bayyana mana babban kalubalen da ka fuskanta, wanda za a iya cewa kamar ta zamar maka wani rigakafi da ciyar da al’umma gaba?

To, a kwana a tashi a cikin tafiyar da lamari na sarauta dole za a sami wasu kalubale. Babban kalubale da zan iya cewa na fuskanta shi ne, a kan matasa maza da mata. Kan lamari na shan kwaya da sace-sace da rashin aiki na samari. To madalla, mun yaki wannan kalubale cikin iko Allah da taimakon gwamnati a lokacin da muka kai kara kuma ya saurare mu. Gwamnati ta yi mana goyon baya da ta taimaka mana muka hassasa wata kungiya da ke bibiyar masu kawo miyagun kwayoyi a cikin Shukura, ana kama su sa’annan kuma ana kama masu shan ta. Kuma ita gwamnatin ta gina mana babban ‘Police Station’ cikin Shukura inda ake jan kunnen masu wannan laifuka. Wannan ya sa muka sami saukin wannan kalubalen ya rage matukar ragewa, kusan ma nace mun rabu da wannan matsalar cikin ikon Allah.

 

Akwai wasu abubuwa da ke faruwa na rikice-rikicen kabilanci, musamman mu a Najeriya, kuma an samu hadin kan al’umma a karkashin masarautarka, maimartaba sarki ta ya ya ka iya cimma hadin kan kabilu daban-daban a masarautarka?

Ma sha Allah, haka ne rikice-rikicen kabilanci ya so ya ci mana gari wani lokaci a baya, amma da ikon Allah mun magance wannan rikice-rikicen. Da farko na yi kiran dukkan sarakan kabilar da ke cikin Zango Shukura da fadawa na kaf, muka tattauna game da samun sulhun wannan al’amari. Sai muka shirya wata kungiya da za mu sami kowane sakin kabila na Shukura ya na ciki kuma da ikon Allah mun kirkiro wannan kungiyar muka sa mata suna (Ablekuma Central Council of Zango Chiefs), amma a karkashin jagoran masarautar Shukura. Wannan kungiyar ta taimaka mana sosai ga samun hadin kan kabilu daban-daban sama da ashirin a Shukura.

 

Ko akwai wasu darusa da ka ke ganin ya kamata masarautunmu na Najeriya su duba su dauka, musamman wurin kan hadin kabilu, ga shi yanzu ana ta fama da rikice-rikice a wasu yankuna da yawa na kasa, kuma ya shafi rikice-rikice ne na cikin al’umma?

Darasi dai da zan iya bayarwa shi ne, kamar yadda muka magance wannan matsalar a kasar mu haka din idan za ku iya yi, to ina ganin za a sami sulhu a wannan rikice-rikicen na kabilanci.

 

A yankin masarautarka mai martaba, wane abu ne ka ke alfahari da shi?

Abin alfaharina na da yawa to, amma zan iya fadin daya, biyu zuwa uku. Na farko na hau kan kujera Shukura babu wuta na lantarki, amma a yanzu ko’ina akwai wutar lantarki duk fadin Shukura. Na biyu zama na a kan karagar mulki na Shukura mun sami ruwa na fanfo a kowane gida. Na uku mun sami hanyoyi na titi masu kyau wanda a da babu. Ga gidan likitoci daban-daban ‘Hospitals’, ‘Police Stations’, makarantu na islamiya da na boko da ma’aikata daban-daban.

 

Mene ne sakon mai martaba sarki ga al’ummar masarautar Shukura da makwaftansu, har ma da dukkan al’ummar Hausawa a duk inda suke a duniya?

Sako na shi ne ayi adalci, rikon amana da tausaya wa talakawa ga dukan dan’adam, balantana ma an dora maka jagorar al’umma a kan ka.

 

Ya ya mai martaba sarki yake ganin alakar gwamnatoci na siyasa da kuma masarautu a kasar Ghana?

Lalle alakar mu sarakuna da gwamnatocin siyasa a kasar mu Ghana na da tsari da aminci sosai. Saboda kodayaushe muka kai kukan mu suna sauraran mu a cikin lumana, girmamawa.

 

Ko akwai abin da mai martaba sarki ke son bayyanawa, wanda ba mu tambaye shi ba?

To abin da yayi saura shi ne, ina yi muku godiya ta musamman da wannan tambayoyin, domin daraja a gare ni da al’ummar Shukura bakidaya. Yadda kuka daraja mu Allah kuma ya daraja ku bakidaya, ya sanya haske a cikin aikin ku da daukaka. Alhaji Armiyawu Sulaiman Sarkin Dandawa na Shukura Ablekuma Central Allah ya kiyaye shi da iyalansa. Allah ya hada hankullan mu bakidaya.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

January 12, 2025
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)
Masarautu

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

July 31, 2024
Next Post
Kwamitin Yaki Da Bala’u Na Sin Ya Kaddamar Da Ayyukan Kandagarki Da Rage Bala’un Lokacin Hunturu Da Bazara

Kwamitin Yaki Da Bala’u Na Sin Ya Kaddamar Da Ayyukan Kandagarki Da Rage Bala’un Lokacin Hunturu Da Bazara

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.