Gwamnatin Tarayya ta gargaɗin game da ambaliyar ruwa, inda ta bayyana cewa al’ummomi da dama a jihohi sama da 30 da Babban Birnin Tarayya na iya fuskantar ambaliya sakamakon mamakon ruwan sama da ake hasashen za a samu tsakanin 22 ga Yuni zuwa 5 ga watan Yulin 2026.
A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya ta fitar, gwamnatin ta ce al’ummomin da ke bakin koguna, yankunan gaɓar ruwa, yankunan da ambaliya ke mamayewa, ƙananan yankuna da kuma wuraren da ba su da ingantattun magudanan ruwa ne suka fi fuskantar barazanar ambaliya.
Daga cikin manyan biranen da aka lissafo akwai Legas, Abuja, Fatakwal, Ibadan, Lokoja, Makurdi, Benin, Enugu, Owerri da Jos.
Ma’aikatar ta sanya Jihar Adamawa cikin jerin jihohin da ke cikin hatsari mafi girma, inda ta yi gargaɗin cewa al’ummomin Yola, Numan, Mubi, Song da sauran yankuna na iya fuskantar mummunar ambaliya, kuma akwai buƙatar su ɗauki matakan gaggawa.
Gwamnatin ta kuma buƙaci mazauna yankunan da ke da hatsarin ambaliya su riƙa sa ido kan matakan ruwa, su share magudanan ruwa da suka toshe, su tanadi hanyoyin neman ɗauki idan ambaliya ta auku, sannan su guji zama ko gudanar da kasuwanci a yankunan da ambaliya ke yawan mamayewa.
Haka kuma, ta buƙaci gwamnatocin jihohi, hukumomin bayar da agajin gaggawa da ƙananan hukumomi su ƙara wayar da kan jama’a tare da ɗaukar matakan shirin ko-ta-kwana domin rage illar ambaliya.














