ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BON Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo Ta Gwamnan Shekara A Fannin Ababen More Rayuwa

by Sulaiman
3 months ago
BON

Hukumar kula da kafafen Watsa Labarai ta Nijeriya (BON), ta karrama Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, da lambar yabo ta “Gwamnan Shekara a Fannin Ababen More Rayuwa,” sakamakon gagarumin ci gaban da gwamnatinsa ta samu musamman a shirin sabunta birane a faɗin jihar.

 

An miƙa wa gwamnan wannan babbar karramawa ne a yayin bugu na biyu na taron BON da aka gudanar a cibiyar taro ta NAF Conference Centre da ke birnin Abuja, inda manyan mutane daga sassa daban-daban suka halarta.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 5, Sun Sace 22 A Sokoto
  • Sabon Salon Nuna Karfin Soja Na Japan Na Sake Haifar Da Barazana 

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa ƙungiyar BON ta yaba da irin sauye-sauyen da ba a taɓa gani ba da gwamnatin Zamfara ta samu a fannin gine-gine da ababen more rayuwa, inda ta nuna cewa wannan karramawa ta wuce fannin watsa labarai kaɗai, tana nuna girmamawa ga nagartattun ayyuka a gwamnati.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sanarwar ta ƙara da cewa, wasu fitattun ‘yan Nijeriya ma sun samu irin wannan karramawa a bikin lambar yabo ta Nigeria Broadcasting Awards na shekarar 2026. Daga cikinsu akwai Gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Otu; Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani; Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Mohammed Idris; tare da wasu fitattun mutane kamar John Momoh, Shyngle Wigwe, Abubakar Jijiwa da kuma Sa’a Ibrahim.

 

Ƙungiyar BON, wadda aka kafa tun a shekarar 1973 domin kare muradun masu watsa labarai da inganta ƙa’idojin aikin jarida a Nijeriya, ta gudanar da tsauraran matakan tantancewa na watanni da dama kafin zaɓen waɗanda suka cancanci wannan karramawa.

 

Kwamitin zaɓen ya kasance ƙarƙashin jagorancin Danladi Bako, tsohon Darakta-Janar na Hukumar Kula da Watsa Labarai ta Ƙasa (NBC), tare da haɗin gwiwar ƙwararru daga National Broadcasting Commission da Advertising Regulatory Council of Nigeria.

 

Kwamitin ya bayyana cewa daga cikin dalilan da suka sa aka zaɓi Gwamna Lawal akwai irin gagarumin cigaban da ya samu a fannoni da dama, musamman yadda ya sauya fasalin birnin Gusau zuwa babban birni na zamani. Haka kuma, an ambaci manyan ayyuka da suka haɗa da gina filin jirgin sama na ƙasa da ƙasa, inganta asibitocin gwamnati, da kuma ginawa da gyara tare da samar da kayan aiki a makarantu sama da 800 a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar.

 

Sanarwar ta jaddada cewa wannan karramawa daga babbar ƙungiyar masu watsa labarai a Nijeriya za ta ƙara wa gwamnan ƙwarin gwiwa wajen ci gaba da jajircewa wajen hidima da sake gina Jihar Zamfara domin al’umma.

BON
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
  • Sulaiman
    Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Mazauna Yankin Sun Tsere Bayan Gano Wasiƙar Kawo Hare-haren Ta’addanci a FCT

’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 1 Tare Da Sace 11 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.