ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BON Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo Ta Gwamnan Shekara A Fannin Ababen More Rayuwa

by Sulaiman
3 months ago
BON

Hukumar kula da kafafen Watsa Labarai ta Nijeriya (BON), ta karrama Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, da lambar yabo ta “Gwamnan Shekara a Fannin Ababen More Rayuwa,” sakamakon gagarumin ci gaban da gwamnatinsa ta samu musamman a shirin sabunta birane a faɗin jihar.

 

An miƙa wa gwamnan wannan babbar karramawa ne a yayin bugu na biyu na taron BON da aka gudanar a cibiyar taro ta NAF Conference Centre da ke birnin Abuja, inda manyan mutane daga sassa daban-daban suka halarta.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 5, Sun Sace 22 A Sokoto
  • Sabon Salon Nuna Karfin Soja Na Japan Na Sake Haifar Da Barazana 

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa ƙungiyar BON ta yaba da irin sauye-sauyen da ba a taɓa gani ba da gwamnatin Zamfara ta samu a fannin gine-gine da ababen more rayuwa, inda ta nuna cewa wannan karramawa ta wuce fannin watsa labarai kaɗai, tana nuna girmamawa ga nagartattun ayyuka a gwamnati.

 

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

Sanarwar ta ƙara da cewa, wasu fitattun ‘yan Nijeriya ma sun samu irin wannan karramawa a bikin lambar yabo ta Nigeria Broadcasting Awards na shekarar 2026. Daga cikinsu akwai Gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Otu; Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani; Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Mohammed Idris; tare da wasu fitattun mutane kamar John Momoh, Shyngle Wigwe, Abubakar Jijiwa da kuma Sa’a Ibrahim.

 

Ƙungiyar BON, wadda aka kafa tun a shekarar 1973 domin kare muradun masu watsa labarai da inganta ƙa’idojin aikin jarida a Nijeriya, ta gudanar da tsauraran matakan tantancewa na watanni da dama kafin zaɓen waɗanda suka cancanci wannan karramawa.

 

Kwamitin zaɓen ya kasance ƙarƙashin jagorancin Danladi Bako, tsohon Darakta-Janar na Hukumar Kula da Watsa Labarai ta Ƙasa (NBC), tare da haɗin gwiwar ƙwararru daga National Broadcasting Commission da Advertising Regulatory Council of Nigeria.

 

Kwamitin ya bayyana cewa daga cikin dalilan da suka sa aka zaɓi Gwamna Lawal akwai irin gagarumin cigaban da ya samu a fannoni da dama, musamman yadda ya sauya fasalin birnin Gusau zuwa babban birni na zamani. Haka kuma, an ambaci manyan ayyuka da suka haɗa da gina filin jirgin sama na ƙasa da ƙasa, inganta asibitocin gwamnati, da kuma ginawa da gyara tare da samar da kayan aiki a makarantu sama da 800 a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar.

 

Sanarwar ta jaddada cewa wannan karramawa daga babbar ƙungiyar masu watsa labarai a Nijeriya za ta ƙara wa gwamnan ƙwarin gwiwa wajen ci gaba da jajircewa wajen hidima da sake gina Jihar Zamfara domin al’umma.

BON
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya
  • Sulaiman
    Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau
  • Sulaiman
    Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

MASU ALAKA

Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aike Da Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi Zuwa Majalisar Dattawa

June 23, 2026
Next Post
Mazauna Yankin Sun Tsere Bayan Gano Wasiƙar Kawo Hare-haren Ta’addanci a FCT

’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 1 Tare Da Sace 11 A Kaduna

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
An Wallafa Litattafan “Zababbun Makaloli Game Da Gina Jam’iyya Na Xi Jinping” Kashi Na 1 Da Na 2

An Wallafa Litattafan “Zababbun Makaloli Game Da Gina Jam’iyya Na Xi Jinping” Kashi Na 1 Da Na 2

June 23, 2026
Wang Yi: Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Mambobin BRICS Don Tinkarar Kalubalen Da Duniya Ke Fuskanta

Wang Yi: Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Mambobin BRICS Don Tinkarar Kalubalen Da Duniya Ke Fuskanta

June 23, 2026
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Tinubu Ya Aike Da Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi Zuwa Majalisar Dattawa

June 23, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2 Tare Da Kama Wasu A Kaduna

June 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Yadda Lakurawa Suka tare Babbar Hanyar Zuwa Neja, Tare Da Jefa Jama’a Cikin Firgici

June 23, 2026
Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.