ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Botswana Ta Yi Barazanar Aika Giwa 20,000 Jamus

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Botswana

Shugaban kasar Botswana ya yi barazanar tura giwa 20,000 zuwa Jamus a wata takaddama a tsakaninta da kasar.

A farkon wannan shekarar ne, ma’aikatar muhalli ta Jamus ta ba da shawarar cewa ka-mata ya yi a tsaurara matakai wajen shigar da lambobin karramawa da aka yi su sassan jikin dabbobin dajin da aka yi farautarsu.

  • Akwai Tashoshin 5G Fiye Da Miliyan 3.5 A Kasar Sin
  • Akwai Tashoshin 5G Fiye Da Miliyan 3.5 A Kasar Sin

Shugaban Botswana Mokgweetsi Masisi ya shaida wa wata kafar yada labaran Jamus cewa matakin zai jefa mutanen kasarsa cikin talauci ne kawai.

ADVERTISEMENT

Ya ce adadin giwaye ya yi yawa ne saboda kokarin alkinta muhalli, farautar kuma tana taimakawa wajen rage adadinsu.

Ya kamata Jamusawa su “zauna tare da dabbobin, kamar yadda kuke kokarin fada ma-na,” in ji shugaba Masisi ga jaridar Jamus Bild. “Wannan ba abin wasa ba ne.”

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Botswana, gida ce ga kusan kashi daya cikin uku na daukacin giwayen duniya – sama da 130,000 – fiye da yadda take da sararin kiwonsu.

Giwayen na yin barna ga dukiyoyi, suna cin amfanin gona tare da tattake mutanen karkara a yankunan, in ji shugaban.

A baya dai, Botswana ta bai wa makwabciyarta Angola giwa 8,000, sannan ta bai wa Mozambikue wasu daruruwan giwaye, a matsayin hanyar rage yawansu a kasar.

“Za mu so mu bayar da irin wannan kyauta ga Jamus,” in ji Masisi, ya kara da cewa ba zai yarda da a’a a matsayin amsa ba.

Ministan namun daji na Botswana Dumezweni Mthhimkhulu a watan da ya gabata ya yi barazanar tura giwaye 10,000 zuwa filin shakatawa na Hyde da ke Landan.
Kungiyoyin kare hakkin dabbobi suna jayayya cewa farautar dabbobi da harbin su san-nan a sarrafa sassan jikinsu kamar kai ko fatarsu, a matsayin lambar karramawa, zalunci ne kuma ya kamata a hana.

Jamus ita ce kasar Tarayyar Turai ta fi shigar da lambobin karramawa da aka yi su da sassan jikin giwa a nahiyar Afirka, a cewar wani rahoto na shekara ta 2021 na kungiyar Humane Society International.

Botswana ta haramta yin hakan a shekarar 2014, amma ta dage haramcin a 2019, bayan fuskantar matsin lamba daga al’ummomin yankin.

A yanzu dai kasar na fitar da kason farautar dabbobi a duk shekara, inda ta ce tana sa-mar da kyakkyawar hanyar samun kudin shiga ga al’ummar yankin, don haka ba su da sha’awar farautar namun daji, kuma tana da lasisi da kuma kula da su sosai.

A baya, an rika amfani da giwaye don yin abincin dabbobi.

Wata mai magana da yawun ma’aikatar muhalli a birnin Berlin ta shaida wa kanfanin dilancin labaren AFP cewa Botswana ba ta nuna damuwa da Jamus kan wannan batu ba.

Ta kara da cewa, “Saboda mummunan asarar da ake samu na bambancin halittu, muna da wani nauyi na musamman na yin komai don tabbatar da cewa shigo da lambobin karramawa da aka yi su sassan jikin giwa na farauta ya dore kuma ya zama doka,” in ji ta.

Ma’aikatar, ta ci gaba da tattaunawa da kasashen Afirka da dokokin shigo da kayayyaki suka shafa, ciki har da Botswana, in ji kakakin.

Ostireliya da Faransa da kuma Belgium na daga cikin kasashen da suka haramta cini-kin lambobin karramawa da aka yi su da sassan jikin giwa da aka yi farauta
A watan Maris, ‘yan majalisar dokokin Burtaniya sun kada kuri’ar amincewa da dokar hana shigo da irin lambobin karramawar nan , amma dokar ta kara yin nazari kafin ta zama doka.

An sanya alkawarin hana shigo da lambobin karramawa da aka yi su da sassan jikin giwa a cikin kundin tsarin zabe na shekarar 2019 na jam’iyyar Conservative.

Ita ma Botswana da makwabciyarta Zimbabwe da Namibiya, sun yi zargin cewa kamata ya yi a bar su su sayar da tarin giwayen da suke da ita, ta yadda za ta samu kudi daga dimbin giwayenta.

Botswana
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?

Kano Pillars: Yaushe Kungiyoyin Kwallon Nijeriya Za Su Daina Shiga Matsalar Kudi?

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.