ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Magance Matsalar Ƙarancin Abinci Mai Gina Jiki A Tsakanin Ƙananan Yara

by Ra'ayinmu
6 months ago
Yara

A bisa ƙoƙarin da ake yi magance ƙalubalen rashin abinci mai gina jiki musamman a tsakanin yara ƙanana da kuma ƙara ƙarafawa iyalai a ɗaukacin faɗin ƙasar nan guwai, hakan ya sanya, a kwnan baya, Sanata Remi Tinubu, mai ɗakin shugaban ƙasa,ta ƙaddamar da wani shiri na ƙasa, domin a magance wannan matsalar.

A jawabinta a yayin ƙaddamarwar Remi da alaƙanta wannan matsalar a matsayin gagarumar matsala wadda ake buƙatar a magance ta, matakin ƙasa, a ƙarƙashin wannan shirin.

  • Shalƙwatar Tsaro Ta Ƙasa Na Shirin Gyaran Tsarin Tubabbun Ƴan Ta’adda
  • Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Hada Kai Wajen Magance Matsalolin Ilimin Yara A Yankunan Da Ake Fama Da Rikici

Shirin dai, za a fara wanzar da shi ne gadan-gadan a cikin watan Afirilun wannan shekarar, wanda kuma aka tsara shi musamman domin inganta samar da abinci mai gina jiki a tsakanin marasa ƙarfi da yara da shekarun su, suka faa daga shekaru shida.

ADVERTISEMENT

A cewar Remi, za a gudanar da shirin ne a hukumomin kiwon kula da kiwon lafiya na farko da ke a ɗaukacin faɗin ƙasar, inda a nan ne, za gudanar da yin rijistar iyalan da aka zaɓo domin amfana da shirin.

Ta ƙara da cewa, waɗanda za su amfana, za a wayar masu da kai da kuma raba masu kayan abinici masu gina jiki da aka noma a ƙasar nan.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Taron ƙadamawar, ya samu halartar Sarakunan Gargajiya, Malaman Addini Ministan kiwon lafiya Farfesa Muhammad Pate ya sanar da cewa, kimanin yara ƙanana kaso 40 a cikin ɗari a ƙasar, na fuskantar matsalar ƙaramcin abinci mai gina jiki, wanda ya ce, wannann matsalar, na fara ne, tun kafin a haifi yaran.

A cewarsa, rashin abinci mai gina jiki, na ƙara haddasa mutuwar yara ƙanana, tun suna gakiyar tasowarsu, da hana su samun ingantaccen ilimi da fuskantar ƙalubale na dogon zango a rayuwarsu.

A bisa ra’ayin mu a wannan Jaridar yaƙar rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara ƙanana a ƙasar abu ne, da yake da matuƙar mahimanci, musamman duba da cewa, a duk makon farko na kowanne watan Agustan shekara, ana gudanar da faɗakarwa ta duniya kan mahimmancin shawar da jarirai Nonon Uwa.

Kazalika, tun kafin a fara fustantar ƙalubalen rashin tsaro a ƙasar, da kuma ɗimbin abincin da ake da shi a ƙasar, yara ƙanana na ci gaba da fuskantar ƙarancin abinci mai gina jiki.

A wasu shekarun baya, Asusun Tallafawa Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya wato UNICEF ta yi haɗaka da shirin samar da abinci wato RUTF na Gwamnatin Tarayya wa, musamman wannan shirin an samar da shi ne, yadda za a rinƙa yin amfani Gyɗar da aka sarrafa, domin magance babbar matsalar ƙarancin abinci mai gina jiki a Arewacin Nijeriya.

Bugu da ƙari, shayar da Jarirai Nonon Uwa zalla, ya ci gaba da kasance kan aƙalla kaso 29 a cikin ɗari, a wan Agustan 2025, inda hakan ya nuna shayarwar, ta ragu da kaso 50 a cikin ɗari, kamar yadda Hukumar Kula da Kiwon Lafiya ta Duniya da Gwamnatin Tarayya, suka ayyana ana son a cimma

A cewar UNICEF, duk da cewa, mata masu shayarwa a ƙasar, sun ƙirƙiro da tsarin shayarwa da ya kao kaso 90 a cikin ɗari, amma har yanzu, ana ci gaba da kai wa wata shida na sahayar da Jarirai Nonon Uwa, wanda hakan ya nuna cewa, akwai buƙatar ƙara samar da tsare-tsare da bayar da goyon baya, a guraren yin aiki yadda mata ma’aikata masu shayarwa, za su samu ƙarin damar shayar da Jariransu, a wajen da suke yin aiki.

A shekaru da dama da suka gabata Gwamnatin Tarayya ta sha ƙiƙiro da ɗauki iri da ban da ban na magance ƙalubalen rashin abinci mai gina jiki, a tsakanin yara ƙanana, sai dai, Gwamnatin na samar da ɗaukin ne kawai, na wucin gadi.

Bugu da ƙari, wannan Jaridar za ta iya tunawa, a shekarar 2025, Gwmantin Tarayya ta ƙiriro da wani shiri na samar da abinci mai gina jiki wanda aka ƙaddamar, a ƙananan hukumomi 774 da ake da su a ƙasar.

Bayan wannan ƙaddamarwar, babban taro na ƙasa na samar sa abinci mai gina jiki da kuma samar da wadataccen abinci, ya biyo baya.

Taron, ya samu halartar ƙwararru daga fannoni da ban da ban, ministoci, hukumomin gwamnati, hukumomin tsaro, Sarakunan Gargajiya, ƴan majalisar taraya da majalisun dokkki da sauran abokan haɗaka.

Mataimakin Shugaban Ƙasa Sanata Kashim Shettima, wanda ya ƙaddamar da buɗe taron ya buƙaci, da samar da dabarun ƙara inganta samar da abinci mai gina jiki da kuma wadataccen abinci a ƙasar.

Sai dai, batun, ba wai kawai halartar Sarakunan Gargajiya da Mlaman Addainai waje ƙaddamarwa bane, akwai kuma matuƙar buƙatar, su ƙara zage damtse wajen faɗaɗar da alumomin su, kan mauhimmancin ciyar da yara ƙanana abinci, mai gina jiki, duba da cewa, ana samun koma baya, wajen ciyar da yaran, waɗanda sune, manyan gobe.

Wannan Jaridar na yin la’akari da cewa, ko da yake kundin tsarin mulkin ƙasar na 1999 da aka sabunta, bai bai wa Sarakunan damar bayar da wata gudunmawa ba, amma suna taimaka wa, wajen wanzar da zaman lafiya da warware rikice-rikice.

Daga watan Afirilun 2025, bisa wasu rahoton da Bankin Duniya ya fitar, sun nuna cewa, aƙalla ƴan Nijeriya kaso 75.5, na ci gaba da zaman cikin talauci.

Bugu da ƙar, yawan masu zama a cikin talauci a karkara, sun ruɓanya yawan mazauna a birne, inda a karkara, ake da kaso 41.3.

Bisa bincken kiwon lafiya da aka gudanar daga 2023 zuwa 2024 na NDHS da kuma fashin baƙin da aka yi a kwanan baya kan ƙarancin abnci mai gina jiki, daga 2024 zuwa 2025, hakan ya nuna cewa, yara ƙanana ƴan shekaru ƙasa da biyar da ke fama da ƙarancin abinci maras jina jiki, da ke zaune a karkara, sun kai sama da kaso 50.

Akwai kuma buƙatar Sarakunan Gargajiya, su rinƙa faɗaɗar musamman mata, kan mahimmancin shayar da Jarirai, Nonon Uwa.

Sai dai, abin damuwar mu shi ne, hujjoji da dama a baya sun nuna cewa, irin wannan ɗaukin da ake samarwa, a ƙarshe, ana yin watsi da shi ne, ba tare da waɗanda ake da burin su amfana ba, sun ci gajiyar ɗaukin ba.

A ƙasar nan, ba wai an gaza samar da tsare-tsare bane, amma matsalar itace, rashin wanzar da tsare-tsaren, yadda ya kamata.

A kwanan baya, an ruwaito shugaba Bola Tinubu ya sanar da cewa, ana samar da ingantacciyar kiwon lafiya, hakan ne zai sanya, a samar da yara manyan gobe, wajen gina ƙasa.

A lokacin yana raye, tsohon shugaban ƙasar Amurka John F. Kennedy, ya bayyana cewa, yara sune babban ginshiƙin yari, a duk faɗin duniya kuma waɗanda ake da babban fana, samar masu

da gobe, mai kyau.

Yara
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Yaƙin Amurka/Israila Da Iran: Gabas Ta Tsakiya Na Tsaka-mai-Wuya

Yaƙin Amurka/Israila Da Iran: Gabas Ta Tsakiya Na Tsaka-mai-Wuya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.