ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

by Sulaiman
4 hours ago
sikila

Amosanin Jini wanda aka fi sani da ciwon Sikila, abu ne da aka shafe shekaru ana fama da ita a cikin alumma, musamman duba da cewa, ana gadon ta ne, a cikin Jiini.

A saboda haka ne, aka keɓe ranar 19, na kowanne watan Juni, domin gudanar da zagoyarwar ranar, domin a tausayawa, masu fama da ita, a ɗaukacin faɗin duniya.

Taken taron na 2026, “ Cike Giɓin da ake Dashi da Baiwa Masu Fama da Cutar kulawar da ta kamata, musamman a ƙasar nan,”.

ADVERTISEMENT

Bincike ya nuna cewa, a Nijeriya, ana da masu fama da ciwon da dama, wanda hakan, ya ɗara na sauran ƙasashen duniya.

Wasu alƙaluma sun nuna cewa, a Nijeriya a duk shekara,  aƙalla ana haihuwar jarirai masu ɗauke da cwon da suka kai yawan150,000

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Wannan adadin, ya nuna cewa, sama da Jariran 100,000 da aka Haifa da ciwon, suna rasuwa, tun kafin su kai matakin binkin su na shekarar haiwa.

Wani abin dubi a nan, shi ne, wannan adadin na Jariran, ba fa wai suna rauswa saboda annobar ƙarancin abinci ko yanayi na yaƙi ba, amma kan lamarin ciwon da za a iya maganinsa, tun bayan da aka haifi Jariran.

Muna taɓa bayyana wa, a wannan shafin cewa, matsalar da fannin kiwon lafiyar ƙasar ke ci gaba da fuskanta, ba wai na rashin samar da kayan kiwon lafiya ba ne, amma batu ne, na rashin samar da kyakywan shugabanci, a ƙasar.

Kazalika, za a iya cewa, shakulatin ɓangaro da gwamnatocin baya da suka mulki ƙasar yi, han ya ƙara sanya ƙaruwar ciwon, a ƙasar.

A gafe ɗaya, idan aka yiwa Gwamnatin mai ci adalaci, a zagowar ranar ta 2026, ta fara gudanar da ranar ce, ta hanyar taron maneman labarai.

Misalili, Ministan Kiwon Lafiya Farfesa Muhammad Ali Pate, a taron na manema labarai, ya bayyana ƙoƙarin da Gwamnatin ke yi, na inganta fannin kiwon lafiyar ƙasar, a ƙarƙashin shirin kula da kiwon lafiya na zuba jari wato RII.

Ya ce, an kafa Cibiyo shida na yaƙar ciwon a shiyyoyin ƙasar, tare da sanya masu kayan aiki na yin gwaje-gwaje, inda ya ƙara da cewa, an samar da tsarin yiwa Jariran da aka haifa gwaji a jihohin Legas, Kano da Abuja.

Ya ci gaba da cewa, an kuma horas da sama da masu bayar da horo, 700 kan sanin Jinsin Jini, inda kuma Ma;aikatasa, ta tantace Jarirai, sama da 38,000 a Abuja, tare da kafa guraren yin rijistar cututtuka guda 10,000 a ɗaukacin Cibiyoyi 25, da ke faɗin ƙasar.

Tabbas, wannan ɗaukar babban matakai ne da suka zo kan gaɓa, na yaƙi da ciwon, wanda hakan, ya sanya muke yabawa Ma’aikatarsa.

Sai dai, a gafe ɗaya, ba za mu yi rashin adalaci, ga masu karanta Jaridar mu ba, musamman duba da yadda miliyoyin ƴan ƙasar 40, musamman waɗanda ke ci gaba da ɗauke da ciwon,  matuƙar ba mu sanar da yawan adadin masu ciwon ba.

Mun ɗora hijjar mu ne, kan cewa, samar da shirin na ƙasa a jihohi uku kacal, tamkar tsoma Allura ce, a cikin Teku, duba da yawan ƙasar ƴan ƙasar, da suka mai sama da miliyan 220, wanda hakan ya nuna a zahiri cewa, waɗanna Cibiyoyin, ko kusa ba su wadaci ƙasar ba.

Kazalika, hakan ya ƙara nuna wa a zahiri, na irin giɓin da ake da shi, a fannin na kiwon lafiyar ƙasar.

Kusan dai, za a iya cewa, a duk matakin Ma’aikatun ƙasar an shafe shekaru, ana tattaunwa kan batun kiwon lafiyar ƙasar, amma har yanzu, lamarin, bai sauya Zani ba.

Wani bincike da Lancet Haematology ya wallafa ya nuna cewa, yaran da ke fama da larurar a ƙasar, sun kai ruɓi huhu, da za su iya mutuwa, kafin su kai shekaru niyar, da haihuwar su

Abin takaicin shi ne,  mahukuntan ƙasar ba su  mayar da hankali, kan ciowan, musamman wajen tattaunawa a matakin ƙasa, musamman lamarin da za a ɗauka, na gaggawa.

Misali,  ana gudanar da yin gamgamin a yi amfani da Ragar gidan Sauro, domin daƙile kamuwa da zazzaɓin cizon Sauro, haka ciwon shan Inna wato Foliyo da cutar Sida, ana ware maƙudan biliyoyin kuɗaɗe a faɗin duniya, domin yaƙar cutar.

Amma abin baƙin ciki  shi ne, larurar ta Sikila da ke hallaka sama da yara ƴan Nijeriya masu shekaru biyar da haihuwa, an mayar da ita Mowa, musamman duba da cewa, idan aka gudanar da taron manema labarai kan gangamin wayar da kai a kanta, daga baya sai kaji, shiru, kamar an shuka Dosa.

Ba za a lumaunci hakan, ya kuma zama wajbi, mahukuntan ƙasar, su sake yin tuninin kan batun.

Abinda aka fi buƙata a  mayar da hankali a yanzu shi ne, dole samar da kuɗaɗe tare da ci gaba da sanya ido, domin a ɗauki, matakan da suka dace, na magance ciwon.

Kazalika, ya zama wajbi, a ƙara faɗaɗa shirin yin gwaji ga Jariran da aka haifa wanda zai wuce, tsayar da shi, a jihiho uku kacal na ƙasar.

Haka zalika, dole a samar da magin rage raɗaɗin ciwon wato Hydroɗyurea, a matakan hukumomin duba lafiya na matakin farko da ke a ɗaukacin faɗin ƙasar.

Dole ne, Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa wato NHISA, ta sanya ciwon na Sikila a cikin jerin jaddawalin da za yiwa masu larurar magani.

Bugu da ƙari, akwai babban nauyin kan matakan gwamnatin jihohi da na ƙananan hukumomi, na su mayar da hankali kan magance ciwon, ta hanyar samar da shirye-shirye.

A ɓangaren ƴan Nijeriya, suma ya zama wajbi a kansu, su cire batun soyayya a gafe, amma su tabbatar da sun je sun yi gwajin sanin Jinsu na Jini, kafin su yi aure.

A ɓanagen guarren ibada, kamar su Masallatai da Ikilisiyya, ya wajaba, su ƙara ƙaimi, wajen jan hankalin mabiyansu, kan mahimmancin yin gwajin Jini, kafin yin aure.

Ba wai za a iya ciki giɓin da ake da shi a ƙasar nan na ciwon bane, ta hanyar yin taron manema labarai, kaɗai ba, inda kuma a gafe ɗaya, a duk shekara ake samu yaran da suka kamu da ciwon 100000, suna rasa rayukansu.

sikila
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
  • Sulaiman
    Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela
  • Sulaiman
    Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
sikila

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.