Amosanin Jini wanda aka fi sani da ciwon Sikila, abu ne da aka shafe shekaru ana fama da ita a cikin alumma, musamman duba da cewa, ana gadon ta ne, a cikin Jiini.
A saboda haka ne, aka keɓe ranar 19, na kowanne watan Juni, domin gudanar da zagoyarwar ranar, domin a tausayawa, masu fama da ita, a ɗaukacin faɗin duniya.
Taken taron na 2026, “ Cike Giɓin da ake Dashi da Baiwa Masu Fama da Cutar kulawar da ta kamata, musamman a ƙasar nan,”.
Bincike ya nuna cewa, a Nijeriya, ana da masu fama da ciwon da dama, wanda hakan, ya ɗara na sauran ƙasashen duniya.
Wasu alƙaluma sun nuna cewa, a Nijeriya a duk shekara, aƙalla ana haihuwar jarirai masu ɗauke da cwon da suka kai yawan150,000
Wannan adadin, ya nuna cewa, sama da Jariran 100,000 da aka Haifa da ciwon, suna rasuwa, tun kafin su kai matakin binkin su na shekarar haiwa.
Wani abin dubi a nan, shi ne, wannan adadin na Jariran, ba fa wai suna rauswa saboda annobar ƙarancin abinci ko yanayi na yaƙi ba, amma kan lamarin ciwon da za a iya maganinsa, tun bayan da aka haifi Jariran.
Muna taɓa bayyana wa, a wannan shafin cewa, matsalar da fannin kiwon lafiyar ƙasar ke ci gaba da fuskanta, ba wai na rashin samar da kayan kiwon lafiya ba ne, amma batu ne, na rashin samar da kyakywan shugabanci, a ƙasar.
Kazalika, za a iya cewa, shakulatin ɓangaro da gwamnatocin baya da suka mulki ƙasar yi, han ya ƙara sanya ƙaruwar ciwon, a ƙasar.
A gafe ɗaya, idan aka yiwa Gwamnatin mai ci adalaci, a zagowar ranar ta 2026, ta fara gudanar da ranar ce, ta hanyar taron maneman labarai.
Misalili, Ministan Kiwon Lafiya Farfesa Muhammad Ali Pate, a taron na manema labarai, ya bayyana ƙoƙarin da Gwamnatin ke yi, na inganta fannin kiwon lafiyar ƙasar, a ƙarƙashin shirin kula da kiwon lafiya na zuba jari wato RII.
Ya ce, an kafa Cibiyo shida na yaƙar ciwon a shiyyoyin ƙasar, tare da sanya masu kayan aiki na yin gwaje-gwaje, inda ya ƙara da cewa, an samar da tsarin yiwa Jariran da aka haifa gwaji a jihohin Legas, Kano da Abuja.
Ya ci gaba da cewa, an kuma horas da sama da masu bayar da horo, 700 kan sanin Jinsin Jini, inda kuma Ma;aikatasa, ta tantace Jarirai, sama da 38,000 a Abuja, tare da kafa guraren yin rijistar cututtuka guda 10,000 a ɗaukacin Cibiyoyi 25, da ke faɗin ƙasar.
Tabbas, wannan ɗaukar babban matakai ne da suka zo kan gaɓa, na yaƙi da ciwon, wanda hakan, ya sanya muke yabawa Ma’aikatarsa.
Sai dai, a gafe ɗaya, ba za mu yi rashin adalaci, ga masu karanta Jaridar mu ba, musamman duba da yadda miliyoyin ƴan ƙasar 40, musamman waɗanda ke ci gaba da ɗauke da ciwon, matuƙar ba mu sanar da yawan adadin masu ciwon ba.
Mun ɗora hijjar mu ne, kan cewa, samar da shirin na ƙasa a jihohi uku kacal, tamkar tsoma Allura ce, a cikin Teku, duba da yawan ƙasar ƴan ƙasar, da suka mai sama da miliyan 220, wanda hakan ya nuna a zahiri cewa, waɗanna Cibiyoyin, ko kusa ba su wadaci ƙasar ba.
Kazalika, hakan ya ƙara nuna wa a zahiri, na irin giɓin da ake da shi, a fannin na kiwon lafiyar ƙasar.
Kusan dai, za a iya cewa, a duk matakin Ma’aikatun ƙasar an shafe shekaru, ana tattaunwa kan batun kiwon lafiyar ƙasar, amma har yanzu, lamarin, bai sauya Zani ba.
Wani bincike da Lancet Haematology ya wallafa ya nuna cewa, yaran da ke fama da larurar a ƙasar, sun kai ruɓi huhu, da za su iya mutuwa, kafin su kai shekaru niyar, da haihuwar su
Abin takaicin shi ne, mahukuntan ƙasar ba su mayar da hankali, kan ciowan, musamman wajen tattaunawa a matakin ƙasa, musamman lamarin da za a ɗauka, na gaggawa.
Misali, ana gudanar da yin gamgamin a yi amfani da Ragar gidan Sauro, domin daƙile kamuwa da zazzaɓin cizon Sauro, haka ciwon shan Inna wato Foliyo da cutar Sida, ana ware maƙudan biliyoyin kuɗaɗe a faɗin duniya, domin yaƙar cutar.
Amma abin baƙin ciki shi ne, larurar ta Sikila da ke hallaka sama da yara ƴan Nijeriya masu shekaru biyar da haihuwa, an mayar da ita Mowa, musamman duba da cewa, idan aka gudanar da taron manema labarai kan gangamin wayar da kai a kanta, daga baya sai kaji, shiru, kamar an shuka Dosa.
Ba za a lumaunci hakan, ya kuma zama wajbi, mahukuntan ƙasar, su sake yin tuninin kan batun.
Abinda aka fi buƙata a mayar da hankali a yanzu shi ne, dole samar da kuɗaɗe tare da ci gaba da sanya ido, domin a ɗauki, matakan da suka dace, na magance ciwon.
Kazalika, ya zama wajbi, a ƙara faɗaɗa shirin yin gwaji ga Jariran da aka haifa wanda zai wuce, tsayar da shi, a jihiho uku kacal na ƙasar.
Haka zalika, dole a samar da magin rage raɗaɗin ciwon wato Hydroɗyurea, a matakan hukumomin duba lafiya na matakin farko da ke a ɗaukacin faɗin ƙasar.
Dole ne, Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa wato NHISA, ta sanya ciwon na Sikila a cikin jerin jaddawalin da za yiwa masu larurar magani.
Bugu da ƙari, akwai babban nauyin kan matakan gwamnatin jihohi da na ƙananan hukumomi, na su mayar da hankali kan magance ciwon, ta hanyar samar da shirye-shirye.
A ɓangaren ƴan Nijeriya, suma ya zama wajbi a kansu, su cire batun soyayya a gafe, amma su tabbatar da sun je sun yi gwajin sanin Jinsu na Jini, kafin su yi aure.
A ɓanagen guarren ibada, kamar su Masallatai da Ikilisiyya, ya wajaba, su ƙara ƙaimi, wajen jan hankalin mabiyansu, kan mahimmancin yin gwajin Jini, kafin yin aure.
Ba wai za a iya ciki giɓin da ake da shi a ƙasar nan na ciwon bane, ta hanyar yin taron manema labarai, kaɗai ba, inda kuma a gafe ɗaya, a duk shekara ake samu yaran da suka kamu da ciwon 100000, suna rasa rayukansu.














