ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Samar Da Cikakken Tsaro Ga Hukumar Zabe Ta INEC

by Leadership Hausa
4 years ago
Tsaro

Daga dukkan alamu akwai wani shiri na musamman daga wasu makiya tsarin dimokuradiyya na ganin sun yi wa kokarin Hukumar Zabe INEC na gudanar da sahihin zabe a shekara mai zuwa zagon kasa.

Hare-haren ban takaidi da ake kaiwa ofishoshin hukumar a sassan kasar a ‘yan wattanin nan alamu ne da ke nuni da hakan.

A makon da ya gabata ne, wasu da ba a kai ga gane ko su wanene ba su ka kai hari tare da kone ofishin INEC a Jihar Ogun bayan sun fi karfin masu gadin ofishin. Rahottanin sun nuna cewa, an lalata ginin ofishin da wasu kayayyakin aiki da suka hada da akwatunan zabe 904, gurbin kebewa don kada kuri’a guda 29, amsa kuwa 30 da jakankunan zabe 57 da kuma teburan zaman jami’an zabe sama da 8, sauran kayan da aka lalata sun hada da katin zabe na dindin 65,699.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kama Wani Guda Daya
  • Gudummawar Kamfanonin Fasahar Sadarwar Kasar Sin Ga Kara Dunkulewar Duniya

Hakanan kuma Kwamishinan zabe na Jihar Osun, Mutiu Agboke, ya sanar da cewa, an banka wa ofishin hukumar da ke karamar hukumar Ede ta Kudu wuta, idan kuma za a iya tunawa ‘yan daba sun kona ofishin INEC da ke karamar hukumar Igbo-Eze a Jihar Inugu da ke yankin Kudu maso Gabashin Nijeriya.

Hukumar ta sanar da cewa, duk da cewa babu wani mutujm da ya rasa ransa amma an lalata akwatunan zabe 748, wurin kebewa don kada kuri’a guda 240, kayayyakin amfani na ofis duk kuwa da kokarin da ofishin kashe gobara na Jihar Inugu daga garin Nsukka yayi don shawo kan gobarar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Bayani ya kuma nuna cewa a watan Afrilu na wannan shekarar, INEC ta sanar da cewa, ta yi asarar na’urar ‘card reader’ da ya fi guda 99,836 a hare-haren da aka kai mata har guda 42 a ofsihoshinta da wadanda aka kai wa ma’aikatanta a cikin shekara uku, haka kuma a wasu bayanai da INEC ta bayar ta sanar da cewa, ya zuwa watan Mayu na shekarar 2021, an kai mata hare-hare da suka kai 41 a jihohi 14 a fadin tayayyar kasar nan a tsakanin shekarar 2019 zuwa 2021. A shekarar 2019 kawai, hukumar zaben ta fuskanci hare- hare 9 a jihohi 4, a shekarar 2020 kuma ta fuskanci hare-hare 21 a jihohi 9, haka kuma a shekarar 2021 an bayar da rahoton hari 11 a jihohi 7 na tarayyar kasar nan. A rahoton, sun ta bayyana cewa, hare-haren ya kunshi kone-kone da lalata mata kayayyaki.

Yadda kone-konen ke kara karuwa a kan ofishoshin INEC da kuma mugun nufin wadanda ke kai hare-haren ya fara tayar da hankulan al’ummar kasa har ana tunanin hare-haren za su iya shafar sahihandin babbar zaben shekarar 2023. Ra’ayin wannan jaridar shi ne lallai wadannan hare-haren a bayyane yake cewa da gangan ne ake yin su da nufin tsorata wasu al’umma daga kada kuri’a tun ma kafin a fara harkar zaben.

A nasu bangaren, kasashen Birtaniya da Amurka sun nuna damuwarsu ga hare-haren da ake kai wa ofisoshin hukumar da yadda ake lalata kayayyanin aiki su a fadin tarayyar kasar nan, sun kuma yi gargadin cewa, lallai wannan babbar barazana de ga zabukkan 2023 kuma barazana de ga ita kanta harkar dimokradiyya da kanta.

Duk da hukumar bata huta ba wajen ganin ta gudanar da sahihin zabe ta hanyar samar da hanyar aika da sakamakon zabe ta na’ura mai kwakwalwa da na’urar BIBAS amma wasu ‘yan siyasa sun dukufa wajen yin zagon kasa ga wannan shiri na hukumar zaben ta hanyar kai hare-hare a kan kayan aikin hukumar INEC musamman a wuraren da suke ganin basu da magoya baya masu yawa, inda suke abokan hamayyar su ne ke da mafi yawan al’ummar da ke a yankin.

Wani karin abin damuwa a nan kuma shi ne mastalar tsaron da ta fuskanta a wasu sassan kasar nan. Muna daukar wadannan matsalolin guda biyu a matsayin abubuwan da za su iya shafar yadda za a gudanar da sahihin zabe cikin kwandiyar hankalin a 2023.

Tuni rahoto ya nuna cewa, akwai wasu al’umma fiye da 686 da suke karkashin ikon ‘yanbindga. Idan za a iya tunawa a watan Yuni na wananan shekarar ne, kungiyar ‘yanta’adda ta Ansaru ta haramta harkokin siyasa a masarautar Birnin Gwari da ke Jihar Kaduna.

Haka kuma matsalar tsaro a yankin Arewandin Nijeriya ya tarwatsa miliyoyin al’umma daga gidajensu na gado. Shugaba Muhammadu Buhari ya umarci jami’an staro su tabbatar da samar da tsaro daga nan zuwa ranar 31 ga watan Disamba. Muna fatan Allah ya basu nasarar samar da cikakiyar zaman lafiya a Nijeriya.

Tabbas mun ji dadin yadda aka samar da karin matakan tsaro a ofishoshin INEC a sassan Nijeriya don kare aukuwar karin hare-haren da ake yi.

Bayani ya nuna cewa, an samar da jami’an ‘yansanda, sojoji, DSS da jami’an hukumar kashe gobara don kare ofishoshin na INEC a sassan Nijeriya. Bugu da kari Babban Sufeton ‘Yansanda, Usman Alkali, ya umarci Kwamishinonin ‘yansanda su samar da shirin tsaro na musamman don kare ofishoshin INEC a fadin tarayyar kasar nan.

A kan wadannan matsololin muke kira ga jami’an tsaro dasu tabbatar da kamawa tare da hukunta dukkan wadanda aka samu da laifin kai hari ofishoshin hukumar zabe na INEC. Tabbas masu kai hare-haren nan ba aljannu ba ne.

Yakamata a tona masu asiri a kuma hukunta su. Suna ci gaba da kai hare-haren ne don babu wanda aka kama aka kuma hukunta. A ra’ayinmu in har aka kai ga kama ‘yansiyasar da ke daukar nauyin masu kai hare-haren tare da hukunta su, to zai taimaka wajen rage hare-haren da ake yi.

A matsayinmu na gidan jarida mun tsaya a kan bukatar gudanar da sahihin zabe a shekarar 2023 da wasu shekarun masu zuwa nan gaba, fatanmu ita de a tabbatar da ra’ayin al’umma de ke yin galaba a zabubbukan da za a gudanar. A ra’ayinmmu kuma daya daga cikin hanyoyin da za a iya dimma wannan burin shi ne tabbatar da cikakken tsaro ga ma’aikata da dukkan kayayyakin zabe da INEC ta tanada.

Tsaro
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Buhari Ya Kafa Tarihi Bayan Shekara 63

Buhari Ya Kafa Tarihi Bayan Shekara 63

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.