Gwamnatin Tarayya ta ba da alamun shirin sake duba mafi ƙarancin albashin ma’aikata na ƙasa, inda ta bayyana cewa ƙa’idar naira 70,000 da ake amfani da ita a yanzu ba ta dace da ainihin halin matsin rayuwa da ake ciki ba.
Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa (Chief of Staff), Femi Gbajabiamila, shi ne ya bayyana haka a birnin Abuja yayin taron tattaunawa kan kyakkyawan shugabanci na shekarar 2026 wanda ƙungiyar Working People United (WoPU) ta shirya.
Gbajabiamila ya jaddada cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu tana sane da yadda farashin kayayyakin masarufi ke ci gaba da tashi, kuma ma’aikata sun cancanci albashin da zai iya ɗaukar nauyin rayuwarsu.
Ya tunatar da cewa a watan Yulin 2024 ne shugaban ƙasar ya sa hannu kan dokar naira 70,000, inda kuma aka rage lokacin sake duba albashin daga shekaru biyar zuwa shekaru uku domin ba da damar gyara shi da sauri idan buƙata ta taso.
Ya ƙara da cewa, duk da cewa adadin naira 70,000 ya kasance babban mataki na canji a lokacin da aka amince da shi, yanayin tattalin arziƙin yau yana buƙatar a sake fuskantar lamarin cikin gaskiya da adalci. Gbajabiamila ya tabbatar wa ƙungiyoyin ƙorafin ma’aikata cewa, idan lokacin sake tattaunawar ya yi, gwamnati ba za ta fuskanci ma’aikata a matsayin abokan gaba ba, face a matsayin abokan haɗin gwuiwar aiki tare.
A nasa ɓangaren, Ministan Kwadago da Samar da Ayyukan Yi, Muhammad Dingyadi, ya bayyana cewa ainihin ma’aunin kyakkyawan shugabanci shi ne yadda tsare-tsaren gwamnati ke fassara zuwa kyautata rayuwar talakawa, da samar da kariya ta zamantakewa, da kuma mutunta ma’aikata.














