Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa har yanzu ba ta karɓi kuɗaɗen da gwamnatin tarayya ta amince a ware mata a kasafin kuɗi domin gudanar da babban zaɓen shekarar 2027 ba.
Shugaban hukumar, Farfesa Joash Amupitan, shi ne ya bayyana haka lokacin da yake kare kasafin kuɗin hukumar a gaban haɗin gwiwar kwamitocin majalisar dattawa da na wakilai kan al’amuran zaɓe a birnin Abuja.
Hukumar ta INEC ta gabatar da gabatar da kasafin kuɗi har na tsabar kuɗi naira biliyan 873.78 domin gudanar da zaɓukan na 2027, inda kwamitin majalisar dattawa ya ma ba da shawarar ƙara naira biliyan 30 a kai domin magance matsalolin masarufi da sufuri.
Shugaban hukumar ya jaddada cewa, dokar zaɓe ta shekarar 2022 ta tanadi cewa dole ne a saki kuɗaɗen zaɓe aƙalla kwanaki 360 kafin ranar zaɓe, domin ba da damar yin kyakkyawan shiri.
Farfesa Amupitan ya bayyana cewa jinkirin sakin kuɗaɗen na iya shafar dabarun tura jami’ai, da samar da kayan aiki, da kuma sabunta tsarin fasahar zamani na hukumar. A halin yanzu, hukumar tana buƙatar kuɗaɗe na musamman domin gudanar da rukunin zaɓukan gwamnoni (off-cycle) a jihohin Ekiti, Osun, da Anambra, waɗanda sune za su zama gwajin farko ga sabbin tsare-tsaren fasahar hukumar kafin babban zaɓen ƙasa baki ɗaya.
A ƙarshe, mambobin kwamitocin majalisar sun nuna goyon bayansu ga hukumar ta INEC tare da yin alƙawarin yin matsin lamba ga ma’aikatar kuɗi ta ƙasa domin ganin an saki kuɗaɗen cikin gaggawa. Sun jaddada cewa samar da kuɗaɗen akan lokaci shi ne kaɗai zai tabbatar da gudanar da zaɓe mai inganci, da sahihanci, da kuma karɓuwa ga dukan al’ummar ƙasar.














