ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ba Tare Da Tangarda Ba A 2025 Ya Karfafa Gwiwar Kasashe Masu Tasowa 

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

A jiya, hukumar kididdiga ta kasar Sin ta gabatar da bayanan tattalin arzikin kasar Sin na shekarar 2025, matakin da ya baiwa duniya wata dama mai kyau ta fahimtar ci gaban Sin. Wannan ba takardar bayanan ci gaban tattalin arzikin kasar Sin ce kadai ba, har ma takarda ce dake karfafa gwiwar kasashe masu tasowa a halin da ake ciki, na rashin tabbas a fannin bunkasar tattalin arzikin duniya. Bayanan sun nuna cewa, a shekara ta 2025, a karon farko GDPn kasar Sin ya wuce Yuan tiriliyan 140, wanda ya karu da kashi 5% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabaci hakan.

Karuwar da Sin ta samu ya zarta hasashen da IMF ta yi kan kasashe masu wadata, wato kashi 1.8% a 2025, ya kuma bayyana rawar da Sin ta taka a fannin ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya. Kamar yadda darektan hukumar kididdiga ta Sin Kang Yi ya jaddada, “ginshikin ingantacciyar bunkasar tattalin arzikin Sin a dogon lokaci bai canja ba.” Ci gaban da Sin take samu na bayyana dorewa, da juriyarta a bangaren raya tattalin arziki, duk da yanayi maras tabbaci, da sarkakiya da ake fuskanta a duniya. Dalilin da ya haifar da hakan shi ne ingantattun ginshikan tattalin arzikinta.

Muna iya ganin hakan a cikin alkaluman da aka fitar, wato tushenta mai inganci, da yin kwaskwarima a gida, bisa dogaro da bunkasar sabbin karfin samar da kayayyaki da hidima mai dorewa.

ADVERTISEMENT

A shekara ta 2025, adadin darajar masana’antar manyan fasahohi a duk fadin kasar Sin ya karu da kashi 9.4%, wanda ya fi bunkasar masana’antu gaba daya sauri. Yawan kayayyakin “sabbin nau’ika uku”, wato motocin lantarki, da batirin lithium, da allunan samar da wutar lantarki ta hasken rana ya karu sosai, inda karuwar motocin lantarki da aka samar ya kai kashi 25.1 %, wadanda suka zama sabon injin dake ingiza bunkasuwar masana’antu. Wannan ba sauye-sauyen masana’antu ne kadai ba, har ma sauye-sauye ne na ci gaba—ci gaban tattalin arziki yana canzawa daga dogaro da tsoffin abubuwa zuwa bunkasa ta hanyar fasaha da kimiyya.

Canjin tsarin tattalin arzikin Sin, musamman bunkasar “sabon karfin samar da kayayyaki da hidimomi masu karko,” ya samar da damammaki ga nahiyar Afirka, wadda ke kokarin samun ci gaban masana’antu da zamanintar da al’umma, kana ma’anar hakan ta zarce batun zuba jari da ciniki kadai, inda ta kai ga samfurin hadin gwiwa, da ci gaban kasashe masu tasowa. Cikakken tsarin hada na’urorin samar da wutar lantarki masu amfani da iska, da hasken rana ta Sin, ya ba da damar yin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, don inganta masana’antu ba tare da gurbata muhalli ba a Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Alal misali, tashoshin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana, da iska da kamfanonin Sin suka gina a Afirka ta Kudu, da Morocco a shekara ta 2025, ba wai kawai sun samar da wutar lantarki mai tsabta ba ce, har ma hakan ya samar da zarafi na hada kayan aiki da horar da ma’aikata da sauransu waje guda, tare da haifar da sabon tsarin masana’antu mai kiyaye muhalli, da dimbin guraben aikin yi.

A shekara ta 2025, duk da rashin karfin raya tattalin arzikin duniya, da bullowar manufar kariyar cinikayya da sauyin yanayi, tattalin arzikin Sin ya nuna halaye na ” ci gaba, da kokarin kirkire-kirkire, da wani yanayi mai karko.” Ainihin karko, ya fito ne daga yin kwaskwarima a gida, da bude kofa ga waje da rungumar sabbin fasahohi. Ta hanyar bunkasa “sabon karfin samar da kayayyaki da hidimomi masu karko,” Sin ta samar da sabon yanayi na tabbas ga kanta da kuma abokan hadin gwiwarta. Ga Afirka, wannan tabbaci yana bayyana cewa, Sin wata abokiyar hadin gwiwa ce mafi kyau.

A sabuwar shekarar nan, duk da cewa tattalin arzikin Sin zai ci gaba da fuskantar kalubaloli daban-daban, ba shakka kasar za ta iya ci gaba da samarwa kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka, da karin damammaki da yanayi na tabbas. (Mai rubuta: MINA)

 

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
gaza

Majalisa Ta Yaba Wa 'Yansanda Kan Gaggawar Kama Waɗanda Ake Zargi Da Kisan Gilla A Kano 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.