ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ba Tare Da Tangarda Ba A 2025 Ya Karfafa Gwiwar Kasashe Masu Tasowa 

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Sin

A jiya, hukumar kididdiga ta kasar Sin ta gabatar da bayanan tattalin arzikin kasar Sin na shekarar 2025, matakin da ya baiwa duniya wata dama mai kyau ta fahimtar ci gaban Sin. Wannan ba takardar bayanan ci gaban tattalin arzikin kasar Sin ce kadai ba, har ma takarda ce dake karfafa gwiwar kasashe masu tasowa a halin da ake ciki, na rashin tabbas a fannin bunkasar tattalin arzikin duniya. Bayanan sun nuna cewa, a shekara ta 2025, a karon farko GDPn kasar Sin ya wuce Yuan tiriliyan 140, wanda ya karu da kashi 5% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabaci hakan.

Karuwar da Sin ta samu ya zarta hasashen da IMF ta yi kan kasashe masu wadata, wato kashi 1.8% a 2025, ya kuma bayyana rawar da Sin ta taka a fannin ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya. Kamar yadda darektan hukumar kididdiga ta Sin Kang Yi ya jaddada, “ginshikin ingantacciyar bunkasar tattalin arzikin Sin a dogon lokaci bai canja ba.” Ci gaban da Sin take samu na bayyana dorewa, da juriyarta a bangaren raya tattalin arziki, duk da yanayi maras tabbaci, da sarkakiya da ake fuskanta a duniya. Dalilin da ya haifar da hakan shi ne ingantattun ginshikan tattalin arzikinta.

Muna iya ganin hakan a cikin alkaluman da aka fitar, wato tushenta mai inganci, da yin kwaskwarima a gida, bisa dogaro da bunkasar sabbin karfin samar da kayayyaki da hidima mai dorewa.

ADVERTISEMENT

A shekara ta 2025, adadin darajar masana’antar manyan fasahohi a duk fadin kasar Sin ya karu da kashi 9.4%, wanda ya fi bunkasar masana’antu gaba daya sauri. Yawan kayayyakin “sabbin nau’ika uku”, wato motocin lantarki, da batirin lithium, da allunan samar da wutar lantarki ta hasken rana ya karu sosai, inda karuwar motocin lantarki da aka samar ya kai kashi 25.1 %, wadanda suka zama sabon injin dake ingiza bunkasuwar masana’antu. Wannan ba sauye-sauyen masana’antu ne kadai ba, har ma sauye-sauye ne na ci gaba—ci gaban tattalin arziki yana canzawa daga dogaro da tsoffin abubuwa zuwa bunkasa ta hanyar fasaha da kimiyya.

Canjin tsarin tattalin arzikin Sin, musamman bunkasar “sabon karfin samar da kayayyaki da hidimomi masu karko,” ya samar da damammaki ga nahiyar Afirka, wadda ke kokarin samun ci gaban masana’antu da zamanintar da al’umma, kana ma’anar hakan ta zarce batun zuba jari da ciniki kadai, inda ta kai ga samfurin hadin gwiwa, da ci gaban kasashe masu tasowa. Cikakken tsarin hada na’urorin samar da wutar lantarki masu amfani da iska, da hasken rana ta Sin, ya ba da damar yin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, don inganta masana’antu ba tare da gurbata muhalli ba a Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Alal misali, tashoshin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana, da iska da kamfanonin Sin suka gina a Afirka ta Kudu, da Morocco a shekara ta 2025, ba wai kawai sun samar da wutar lantarki mai tsabta ba ce, har ma hakan ya samar da zarafi na hada kayan aiki da horar da ma’aikata da sauransu waje guda, tare da haifar da sabon tsarin masana’antu mai kiyaye muhalli, da dimbin guraben aikin yi.

A shekara ta 2025, duk da rashin karfin raya tattalin arzikin duniya, da bullowar manufar kariyar cinikayya da sauyin yanayi, tattalin arzikin Sin ya nuna halaye na ” ci gaba, da kokarin kirkire-kirkire, da wani yanayi mai karko.” Ainihin karko, ya fito ne daga yin kwaskwarima a gida, da bude kofa ga waje da rungumar sabbin fasahohi. Ta hanyar bunkasa “sabon karfin samar da kayayyaki da hidimomi masu karko,” Sin ta samar da sabon yanayi na tabbas ga kanta da kuma abokan hadin gwiwarta. Ga Afirka, wannan tabbaci yana bayyana cewa, Sin wata abokiyar hadin gwiwa ce mafi kyau.

A sabuwar shekarar nan, duk da cewa tattalin arzikin Sin zai ci gaba da fuskantar kalubaloli daban-daban, ba shakka kasar za ta iya ci gaba da samarwa kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka, da karin damammaki da yanayi na tabbas. (Mai rubuta: MINA)

 

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
gaza

Majalisa Ta Yaba Wa 'Yansanda Kan Gaggawar Kama Waɗanda Ake Zargi Da Kisan Gilla A Kano 

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Sin

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Sin

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.