ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cinikayyar Sin Da Afirka Ta Bude Sabon Babi

by Sulaiman
8 months ago
Sin

Hukumar kwastam ta kasar Sin, ta fitar da wasu bayanan cinikayyar shige da fice ta Sin na shekarar 2025 a jiya Alhamis. Alkaluman na nuna cewa, darajar cinikin shige da fice tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, ya kai yuan tiriliyan 2.49, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 357.076, adadin da ya wuce dala biliyan 300 a karon farko, kana ya karu da kashi 18.4 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabaci hakan. Daga cikin kasashe 64 na Afirka da Sin ke cinikayya da su, yawan karuwar ciniki da kasashe 41 ya kai fiye da kashi 10 cikin 100, yayin da kasashe 22 suka samu karuwar fiye da kashi 30 cikin 100.

A bangaren shigo da kayayyaki, Sin tana aiwatar da matakin janye haraji kashi 100 cikin 100, kan kayayyakin da ake shigar da su kasar, daga kasashe 53 na Afirka masu huldar diplomasiyya da ita, don fadada shigo da kayayyakinsu cikin gidanta, da kuma raba fa’idar babbar kasuwar Sin. Wannan ya sa kayayyakin amfanin gona masu karin daraja irin su avocado na Kenya, da kofi na Habasha, da lemun tsami na Afirka ta Kudu, samun damar kara shiga kasuwar Sin, wanda hakan ke amfanar da manoma, da kananan kamfanoni na Afirka.

A bangaren fitar da kayayyaki, kayayyakin da Sin ke fitarwa zuwa Afirka ya inganta sosai. Inda cinikin wasu kayayyaki masu kunshe da fasahar zamani, irin su sabbin motoci masu amfani da wutar lantarki, da na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana, da batirin lithium, ke cikin wani yanayi na karuwa. Ban da haka, kayayyakin Sin suna taimakawa wajen inganta masana’antu, da kuma yunkurin karkata zuwa sabon salon bunkasa ba tare da gurbata muhalli ba a Afirka.

ADVERTISEMENT

Bayanan cinikayya na shekarar 2025, takarda ce mai nauyi da ke bayyana nasarorin da aka samu, kuma takardar ta fayyace alkawarin da Sin take cikawa, na samun ci gaba tare da kasashen waje, har ma takardar ta sanar da makoma mai haske a nan gaba. Kazalika, ta bayyana hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, da dogaro da juna, da daidaito, da cin moriyar juna, da daukar ainihin matakai, wanda hakan ke taimakawa wajen habaka tattalin arzikin duniya, da kuma kyautata tsarin shugabancin duniya.

Tattaunawa tsakanin Sin da kungiyar tarayyar Afirka ta AU kan manyan tsare-tsare da aka kammala a kwanan nan, ya tabbatar da karfafa hadin kai tsakanin shirin ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sin na shekaru biyar-biyar karo na 15, da shirin “Raya Afirka nan da 2063” na AU, wanda hakan shaida ce mafi kyau ga yunkurin bangarorin Sin da Afirka na samun ci gaba tare.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Idan an yi hangen nesa, za a ga cewa kasar Sin da kasashen nahiyar Afirka, bisa hadin gwiwarsu za su kirkiro wani sabon tsari na tattalin arzikin duniya, mai tabbatar da daidaito da wadata tsakanin dimbin bangarori masu fada-a-ji. (Mai rubuta: MINA)

 

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Kotu Ta Janye Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Sanata Natasha

Kotu Ta Janye Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Sanata Natasha

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.