ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cinikayyar Sin Da Afirka Ta Bude Sabon Babi

by Sulaiman
6 months ago
Sin

Hukumar kwastam ta kasar Sin, ta fitar da wasu bayanan cinikayyar shige da fice ta Sin na shekarar 2025 a jiya Alhamis. Alkaluman na nuna cewa, darajar cinikin shige da fice tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, ya kai yuan tiriliyan 2.49, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 357.076, adadin da ya wuce dala biliyan 300 a karon farko, kana ya karu da kashi 18.4 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabaci hakan. Daga cikin kasashe 64 na Afirka da Sin ke cinikayya da su, yawan karuwar ciniki da kasashe 41 ya kai fiye da kashi 10 cikin 100, yayin da kasashe 22 suka samu karuwar fiye da kashi 30 cikin 100.

A bangaren shigo da kayayyaki, Sin tana aiwatar da matakin janye haraji kashi 100 cikin 100, kan kayayyakin da ake shigar da su kasar, daga kasashe 53 na Afirka masu huldar diplomasiyya da ita, don fadada shigo da kayayyakinsu cikin gidanta, da kuma raba fa’idar babbar kasuwar Sin. Wannan ya sa kayayyakin amfanin gona masu karin daraja irin su avocado na Kenya, da kofi na Habasha, da lemun tsami na Afirka ta Kudu, samun damar kara shiga kasuwar Sin, wanda hakan ke amfanar da manoma, da kananan kamfanoni na Afirka.

A bangaren fitar da kayayyaki, kayayyakin da Sin ke fitarwa zuwa Afirka ya inganta sosai. Inda cinikin wasu kayayyaki masu kunshe da fasahar zamani, irin su sabbin motoci masu amfani da wutar lantarki, da na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana, da batirin lithium, ke cikin wani yanayi na karuwa. Ban da haka, kayayyakin Sin suna taimakawa wajen inganta masana’antu, da kuma yunkurin karkata zuwa sabon salon bunkasa ba tare da gurbata muhalli ba a Afirka.

ADVERTISEMENT

Bayanan cinikayya na shekarar 2025, takarda ce mai nauyi da ke bayyana nasarorin da aka samu, kuma takardar ta fayyace alkawarin da Sin take cikawa, na samun ci gaba tare da kasashen waje, har ma takardar ta sanar da makoma mai haske a nan gaba. Kazalika, ta bayyana hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, da dogaro da juna, da daidaito, da cin moriyar juna, da daukar ainihin matakai, wanda hakan ke taimakawa wajen habaka tattalin arzikin duniya, da kuma kyautata tsarin shugabancin duniya.

Tattaunawa tsakanin Sin da kungiyar tarayyar Afirka ta AU kan manyan tsare-tsare da aka kammala a kwanan nan, ya tabbatar da karfafa hadin kai tsakanin shirin ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sin na shekaru biyar-biyar karo na 15, da shirin “Raya Afirka nan da 2063” na AU, wanda hakan shaida ce mafi kyau ga yunkurin bangarorin Sin da Afirka na samun ci gaba tare.

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Idan an yi hangen nesa, za a ga cewa kasar Sin da kasashen nahiyar Afirka, bisa hadin gwiwarsu za su kirkiro wani sabon tsari na tattalin arzikin duniya, mai tabbatar da daidaito da wadata tsakanin dimbin bangarori masu fada-a-ji. (Mai rubuta: MINA)

 

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi
  • Sulaiman
    Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC
  • Sulaiman
    Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Next Post
Kotu Ta Janye Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Sanata Natasha

Kotu Ta Janye Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Sanata Natasha

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.