ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cinikayyar Sin Da Afirka Ta Bude Sabon Babi

by Sulaiman
5 months ago
Sin

Hukumar kwastam ta kasar Sin, ta fitar da wasu bayanan cinikayyar shige da fice ta Sin na shekarar 2025 a jiya Alhamis. Alkaluman na nuna cewa, darajar cinikin shige da fice tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, ya kai yuan tiriliyan 2.49, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 357.076, adadin da ya wuce dala biliyan 300 a karon farko, kana ya karu da kashi 18.4 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabaci hakan. Daga cikin kasashe 64 na Afirka da Sin ke cinikayya da su, yawan karuwar ciniki da kasashe 41 ya kai fiye da kashi 10 cikin 100, yayin da kasashe 22 suka samu karuwar fiye da kashi 30 cikin 100.

A bangaren shigo da kayayyaki, Sin tana aiwatar da matakin janye haraji kashi 100 cikin 100, kan kayayyakin da ake shigar da su kasar, daga kasashe 53 na Afirka masu huldar diplomasiyya da ita, don fadada shigo da kayayyakinsu cikin gidanta, da kuma raba fa’idar babbar kasuwar Sin. Wannan ya sa kayayyakin amfanin gona masu karin daraja irin su avocado na Kenya, da kofi na Habasha, da lemun tsami na Afirka ta Kudu, samun damar kara shiga kasuwar Sin, wanda hakan ke amfanar da manoma, da kananan kamfanoni na Afirka.

A bangaren fitar da kayayyaki, kayayyakin da Sin ke fitarwa zuwa Afirka ya inganta sosai. Inda cinikin wasu kayayyaki masu kunshe da fasahar zamani, irin su sabbin motoci masu amfani da wutar lantarki, da na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana, da batirin lithium, ke cikin wani yanayi na karuwa. Ban da haka, kayayyakin Sin suna taimakawa wajen inganta masana’antu, da kuma yunkurin karkata zuwa sabon salon bunkasa ba tare da gurbata muhalli ba a Afirka.

ADVERTISEMENT

Bayanan cinikayya na shekarar 2025, takarda ce mai nauyi da ke bayyana nasarorin da aka samu, kuma takardar ta fayyace alkawarin da Sin take cikawa, na samun ci gaba tare da kasashen waje, har ma takardar ta sanar da makoma mai haske a nan gaba. Kazalika, ta bayyana hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, da dogaro da juna, da daidaito, da cin moriyar juna, da daukar ainihin matakai, wanda hakan ke taimakawa wajen habaka tattalin arzikin duniya, da kuma kyautata tsarin shugabancin duniya.

Tattaunawa tsakanin Sin da kungiyar tarayyar Afirka ta AU kan manyan tsare-tsare da aka kammala a kwanan nan, ya tabbatar da karfafa hadin kai tsakanin shirin ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sin na shekaru biyar-biyar karo na 15, da shirin “Raya Afirka nan da 2063” na AU, wanda hakan shaida ce mafi kyau ga yunkurin bangarorin Sin da Afirka na samun ci gaba tare.

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Idan an yi hangen nesa, za a ga cewa kasar Sin da kasashen nahiyar Afirka, bisa hadin gwiwarsu za su kirkiro wani sabon tsari na tattalin arzikin duniya, mai tabbatar da daidaito da wadata tsakanin dimbin bangarori masu fada-a-ji. (Mai rubuta: MINA)

 

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Next Post
Kotu Ta Janye Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Sanata Natasha

Kotu Ta Janye Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Sanata Natasha

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.