Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya umarci dakarun rundunar haɗin gwiwa ta yankin Arewa ta Tsakiya (JTF-NC), ‘Operation Savannah Shield’, da su murƙushe ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka da ke ta’addanci a Jihar Kwara da jihohin maƙwabta.
Hafsan sojin ya kuma umurci dakarun da su ƙara ƙaimi a ayyukan da suke gudanarwa domin kawo ƙarshen masu tayar da zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.
A cikin wata sanarwa da Mukaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Ƙasa, Kanal Apollonia Anele, ya fitar, ta ce COAS ya bayar da umarnin ne yayin da yake jawabi ga dakaru a Barikin Sobi da ke Ilorin, a ziyararsa ta farko ta aiki zuwa hedikwatar rundunar ‘JTF North Central Operation Savannah Shield’ a Jihar Kwara.
Yayin jawabin nasa ga dakarun, Laftanar Janar Waidi ya jaddada cewa Rundunar Sojin Nijeriya na ci gaba da jajircewa wajen sauke nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora mata na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin ƙasar nan.
Ya bayyana cewa dakarun sun ci gaba da gudanar da ayyuka cikin ƙwazo domin hana masu aikata laifuka damar ci gaba da addabar mutane, kutsawa cikin al’umma ko kuma kawo barazana ga tsaron ƙasa.















Discussion about this post