ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Ne Annabi Muhammad (SAW) Ba Ya Kashe Wanda Ya Zage Shi?

by Sulaiman
4 years ago

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

Mutane da yawa musamman ‘yan boko akida suna ta tambaya suna cewa: “Babu wani hadisi ingantacce da Annabi (SAW) ya kashe wanda ya zage shi, hasalima akwai wadanda suka aibata Annabi a gabansa, suka zage shi amma bai kashe su, bai Kuma yi umarni da kashe su ba, don Allah malam Ya abin yake, kuma sahabbai ba su far musu ba”?
Wa alaikum assalam. Allah Yana cewa a cikin suratul Ahzaab aya ta (57): “Tabbas wadanda suke cutar da Allah da Mazonsa Allah Ya la’ance su a duniya da lahira Kuma ya tanazar musu da azaba wulakantacciya”
Ka’ab dan Al’ashraf ya kasance yana cutar da Annabi (SAW), sai Manzon tsira ya shelanta cewa wa zai isar masa game da wannan cutarwar da ake masa? Sai Muhammad dan Maslama ya ce ya Manzon Allah kana so na kashe shi? Sai ya ce na’am, sai ya tafi gidansa shi da tawagarsa, suka aika shi lahira, bayan ya yi sabuwar Amarya daga babban gida, Kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi Mai lamba ta (3811).
Annabi (SAW) ya samu labarin wani Makaho da ya kashe baiwarsa cikin dare, sai ya tambaye shi me ya sa ka yi haka? Sai ya ce ta kasance mai tausasawa gare ni, Kuma ina da kyawawan yara da ta haifa mini, amma Kuma tana aibanta ka, nakan hana ta, amma sai ta ki hanuwa, jiya da daddare na ji ta tana aibanta ka sai na samo adda sai na dankara a cikinta, na danna har ta mutu, dan da yake cikinta ya bulluko, sai Annabi (SAW) ya ce : “Ku shaida tabbas jininta ya ta fi a banza”, Abu Dawud ya rawaito shi kuma Albani ya inganta shi a hadisi Mai lamba ta (4361).
Ire-iren wadannan hadisan suna da yawa, suna tabbatar da aika duk wanda ya zagi Annabi (SAW) zuwa Lahira .
Tabbas akwai munafukan da suke aibanta Annabi (SAW) a zamaninsa kamar yadda ya zo a suratu Attauba da kuma suratu Almunafikun, amma bai kashe su ba, saboda mutanen da suke gefe za su ce Muhammad yana kashe sahabbansa, saboda ba za su bambance tsakanin wanda ya shiga Musulunci da wasa ba da kuma wanda ya shiga da gaske, saboda wannan maslahar Annabi (SAW) ya kyale su, don toshe barnar da za ta iya hana wasu shiga Musulunci.
Idan mutum ya ga wanda ya zagi Annabi (SAW) bai iya jurewa ba har jami’an tsaro su karaso, ya aika shi Barzahu saboda fusata da kuma son sa ga Manzon Tsira, jinin wanda aka kashen ya tafi a banza, babu kisasi, mutukar zagin da ya yi da gangan ne, ba shi da tawili ko shubuhar da ta kasa warwaruwa, in kuma ya bayyana ba zaginsa ya yi ba, to sai ya biya rabin diyyar Musulmi, amma ba za a kashe shi ba.
Allah ne mafi sani.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

May 29, 2026
Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
Dausayin Musulunci

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

May 22, 2026
Dausayin Musulunci

Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci

May 15, 2026
Next Post
Aikin Hajji Da Hukuncin Tsallake Mikati Ba Tare An Yi Harama Ba

Aikin Hajji Da Hukuncin Tsallake Mikati Ba Tare An Yi Harama Ba

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.