Tun daga karuwar hada-hadar albarkatun gona masu inganci da ake shigarwa kasar Sin daga sassan nahiyar Afirka, da cinikayyar na’urorin samar da makamashi kirar Sin dake kara samun kasuwa a sassan Afirka, zuwa harkokin gine-ginen zamani na Sin masu taimakawa ci gaban ababen more rayuwa a kasashen Afirka, muna iya fahimtar ci gaban da hada-hadar cinikayya tsakanin Sin da Afirka ke kara haifarwa ga bangarorin biyu.
A shekarun baya bayan nan, tsarin cinikayya tsakanin Sin da nahiyar Afirka na kara kyautata. Wasu alkaluma da hukumar kwastam ta Sin ta fitar sun tabbatar da cewa, a cikin watanni 6 na farkon shekarar bana, darajar cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka ta kai kudin Sin tiriliyan 1.41 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 208, wanda ya kafa matsayin tarihi.
Wannan muhimmin mataki na tarihi na da matukar kima, ba kawai ta fuskar adadin kudaden cinikayya ba, har ma da muhimmin fannin sauyin tsarin cinikayyar sassan biyu. Musamman duba da yadda kasashen Afirka ke kara samun zarafi na fitar da tarin hajojinsu zuwa kasar Sin, wanda hakan ke nuni ga inganci, da kuma yalwar hajojin da nahiyar ke samarwa, yayin da karuwar shigar da hajojin Sin cikin nahiyar, wadanda suka hada da na fasahohi, da na ayyukan masana’antu ke shaida karin karbuwar hajojin Sin masu tallafawa ci gaban Afirka a tsakanin al’ummun nahiyar. Tabbas, sakamakon wannnan ci gaba a bayyane yake, wato hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ya ginu ne kan tsari na cude-ni-in-cude-ka, yayin da kasuwannin sassan biyu ke kara dinkewa da dunkulewa waje guda.
A gabar da ake cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka a bana, Sin ta kaddamar da manufar soke harajin fito kan hajojin kasashen Afirka 53 da ke da huldar diflomasiyya da ita. Wanda hakan ya sanya Sin din zama babbar kasa a duniya ta farko da ta aiwatar da irin wannan manufa mai matukar alfanu ga al’ummun Afirka.
Yayin da tsarin cinikayyar kasa da kasa ke sauya salo, kuma wasu sassa ke daukar matakai na kariyar cinikayya, Sin na ci gaba da fadada bude kofofinta ga nahiyar Afirka. Kuma wadannan matakai sun samar da karin dama ta daidaituwar yanayin kasuwa, da karin damarmakin fadada hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka. (Saminu Alhassan)














