Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce Amurka ta kai wa Iran hari ne domin kare kanta, kada Iran ta rama harin da Isra’ila ta kai mata.
Trump ya bayyana hakan ne yayin ganawa da shugaban gwamnatin Jamus, Friedrich Merz.
- SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 15
- Kotu Ta Ƙi Amincewa Da Bukatar Tsoffin Kwamishinonin Kano Na Riƙe Motocin Gwamnati
Ya ce shugabannin Iran suna cikin fushi, kuma Amurka na da isassun makamai da za ta iya ci gaba da yaƙi na tsawon lokaci.
Duk da haka, ya ce baya son yaƙin ya wuce makonni huɗu zuwa biyar.
Trump ya kuma yi barazanar dakatar da hulɗar kasuwanci da Spain, saboda ƙin amincewa da amfani da ƙasarta wajen kai wa Iran hari, da kuma saɓanin da suke da ita kan ƙungiyar NATO.
A nasa ɓangaren, Merz ya nuna goyon bayansa ga matakin da Amurka da Isra’ila suka ɗauka, amma ya ce yana fatan a kawo ƙarshen yaƙin cikin gaggawa.
Ya bayyana cewa yaƙin yana cutar da tattalin arziƙin duniya, musamman ta fuskar tashin farashin man fetur da iskar gas.
Rahotanni daga Iran sun ce sama da mutane 780 sun mutu cikin kwanaki huɗu na fafatawar.
Rikicin ya bazu zuwa wasu ƙasashen Gabas ta Tsakiya, inda Iran ta kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka da wasu wuraren tsaro.
Hare-haren sun sa an rufe wasu matatun mai, lamarin da ya jawo ƙarin tashin farashin mai a kasuwannin duniya.















Discussion about this post