Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa kuma tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida, Abdulrahman Dambazau, ya karɓi aiki a hukumance a matsayin Jakadan Nijeriya zuwa China, inda ya fara gudanar da ayyukansa a ofishin jakadancin Nijeriya da ke birnin Beijing.
Bayan isarsa ofishin jakadancin ranar 28 ga Mayu, 2026, Dambazau ya gana da jami’an ofishin kafin ya fara gudanar da ayyukansa a matsayin shugaban tawagar jakadancin Nijeriya a ƙasar China.
A cewar sanarwar, sabon jakadan ya nuna aniyarsa ta inganta dangantakar da ke tsakanin Nijeriya da China tare da bunƙasa haɗin gwuiwa a fannoni daban-daban da za su amfani ƙasashen biyu.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne ya naɗa Dambazau cikin jerin jakadun da ba ma’aikatan harkokin diflomasiyya ba a watan Disambar 2025. Daga bisani Majalisar Dattijai ta amince da naɗin nasa kafin a tura shi ƙasar China a watan Maris na 2026.















Discussion about this post