Tsohon Gwamnan Jihar Gombe kuma Sanata mai wakiltar Gombe ta Tsakiya, Mohammed Danjuma Goje, ya musanta rahotannin da ke cewa ya karɓi katin zama ɗan Jam’iyyar ADC, yana mai jaddada cewa har yanzu yana cikakken mamba na jam’iyyar APC.
Goje ya bayyana kansa a matsayin “ɗan APC mai alfahari,” inda ya ƙaryata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke alaƙanta shi da komawa sabuwar haɗakar siyasa ta adawa.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ƙara samun yaɗuwar jita-jitar sauya sheƙa a fagen siyasar Najeriya gabanin zaɓen 2027.
Sai dai masu magana da yawunsa sun ce Goje bai fice daga APC ba, kuma yana ci gaba da halartar harkokin jam’iyyar a matakin ƙasa.
Masu nazari sun ce irin wannan jita-jita kan yawaita a lokacin da ake tunkarar manyan zaɓe, amma ba koyaushe take da tushe ba.















Discussion about this post