ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Doguwa Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Kano

by Sadiq
6 months ago
APC

Umar Haruna Doguwa ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano bayan an cimma matsaya da aka yi a taron jam’iyyar da aka gudanar a daren ranar Talata.

Doguwa ya taɓa riƙe wannan muƙami kimanin shekaru 10 da suka gabata.

  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 15
  • Kafar CGTN Ta Fitar Da Rahoto Game Da Hasashen Ababen Mayar Da Hankali Yayin Manyan Taruka Biyu Na Sin

An tabbatar da shi ne a taron da aka yi a filin wasa Sani Abacha, inda wakilai daga ƙananan hukumomi 44 na jihar suka halarta.

ADVERTISEMENT

Shugaban kwamitin gudanar da taron, Rabiu Suleiman Bichi, ya ce an cike dukkanin muƙamai ta hanyar yin sulhu.

Ya bayyana cewa wakilai kusan 2,400 ne suka halarci taron, kuma duk sun amince da shugabannin da aka zaɓa ba tare da wata adawa ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Sauran waɗanda aka zaɓa sun haɗa da Salisu Maje Ahmed Gwangwazo a matsayin Mataimakin Shugaba, Farfesa Yusuf Muhammad Sabo Bichi a matsayin Sakatare, da Farfesa Nura Yaro Dawakin Tofa a matsayin Mataimakin Sakatare.

Haka kuma an zaɓi wasu domin riƙe sauran muƙamai domin tafiyar da harkokin gudanarwa.

An rantsar da sabbin shugabannin tare da kira a gare su da su bi kundin tsarin mulkin jam’iyyar tare da yin aiki cikin haɗin kai.

A jawabinsa na karɓar muƙamin, Doguwa ya gode wa shugabanni da wakilai bisa amincewar da suka nuna masa.

Ya yi alƙawarin tafiyar da shugabanci domin ƙoƙarin ƙarfafa jam’iyya gabanin zaɓuka masu zuwa.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya taya sabbin shugabannin murna, yana mai cewa zaman lafiya da aka samu a taron alama ce ta ci gaban siyasa.

Ya buƙace su da su tabbatar da adalci, haɗin kai da dimokuraɗiyya a cikin harkokin jam’iyya.

Manyan ’yan siyasa da suka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin, Tijjani Abdullahi Gwarzo, Abdussalam Abdulkarim Zaura da Murtala Sule Garo, da sauransu.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

DSS Ta Kama Wasu Jami’an Tsaro Kan Zargin Taimaka Wa El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.