ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Doguwa Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Kano

by Sadiq
4 months ago
APC

Umar Haruna Doguwa ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano bayan an cimma matsaya da aka yi a taron jam’iyyar da aka gudanar a daren ranar Talata.

Doguwa ya taɓa riƙe wannan muƙami kimanin shekaru 10 da suka gabata.

  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 15
  • Kafar CGTN Ta Fitar Da Rahoto Game Da Hasashen Ababen Mayar Da Hankali Yayin Manyan Taruka Biyu Na Sin

An tabbatar da shi ne a taron da aka yi a filin wasa Sani Abacha, inda wakilai daga ƙananan hukumomi 44 na jihar suka halarta.

ADVERTISEMENT

Shugaban kwamitin gudanar da taron, Rabiu Suleiman Bichi, ya ce an cike dukkanin muƙamai ta hanyar yin sulhu.

Ya bayyana cewa wakilai kusan 2,400 ne suka halarci taron, kuma duk sun amince da shugabannin da aka zaɓa ba tare da wata adawa ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Sauran waɗanda aka zaɓa sun haɗa da Salisu Maje Ahmed Gwangwazo a matsayin Mataimakin Shugaba, Farfesa Yusuf Muhammad Sabo Bichi a matsayin Sakatare, da Farfesa Nura Yaro Dawakin Tofa a matsayin Mataimakin Sakatare.

Haka kuma an zaɓi wasu domin riƙe sauran muƙamai domin tafiyar da harkokin gudanarwa.

An rantsar da sabbin shugabannin tare da kira a gare su da su bi kundin tsarin mulkin jam’iyyar tare da yin aiki cikin haɗin kai.

A jawabinsa na karɓar muƙamin, Doguwa ya gode wa shugabanni da wakilai bisa amincewar da suka nuna masa.

Ya yi alƙawarin tafiyar da shugabanci domin ƙoƙarin ƙarfafa jam’iyya gabanin zaɓuka masu zuwa.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya taya sabbin shugabannin murna, yana mai cewa zaman lafiya da aka samu a taron alama ce ta ci gaban siyasa.

Ya buƙace su da su tabbatar da adalci, haɗin kai da dimokuraɗiyya a cikin harkokin jam’iyya.

Manyan ’yan siyasa da suka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin, Tijjani Abdullahi Gwarzo, Abdussalam Abdulkarim Zaura da Murtala Sule Garo, da sauransu.

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

DSS Ta Kama Wasu Jami’an Tsaro Kan Zargin Taimaka Wa El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.