ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dokar Tsaron Kasa Ta Yi Kyakkyawan Tasiri A Yankin Hong Kong

by CGTN Hausa
3 years ago
Hong Kong

Sanin kowa ne cewa, kiyaye tsaron kasa, batu ne da ya shafi muhimman muradun kowace kasa a duniya. Kuma tun bayan da yankin musamman na Hong Kong ya dawo karkashin ikon kasar Sin, bisa ka’ida ta 23 cikin babbar dokar yankin, gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta dankawa yankin izinin kafa dokarsa ta fannin kiyaye tsaron kasa.

Sai dai kafin kafa dokar, yankin ya fuskanci wasu ayyuka na rashin doka a bangaren tsaron kasa wanda masana ke cewa, ba ya rasa nasaba da tsoma baki a harkokin yankin daga ketare.

Idan ba a manta ba a shekarar 2019, wasu bata-gari suka yi yunkurin balle Hong Kong daga kasar Sin, da cin zarafi gami da lalata tambari da tutar kasa, da zuga al’umma don su mamaye ofishin gwamnatin tsakiya dake Hong Kong, da kai hari kan mai uwa da wabi, da cin zarafin ’yan sanda wadanda a kullum suke sadaukar da rayukansu don tabbatar da tsaron al’umma, al’amuran da suka kasance ayyukan ta’addanci, da haifar da babbar barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a Hong Kong gami da cikakken iko na kasa.

ADVERTISEMENT

Kuma duk wata kasa da ta san abin da take yi, ba za ta amince da irin wannan danyen aiki ba. Bayan kafa wannan doka, a makon nan aka yi nasarar gudanar da zaben ’yan majalisar kafa dokoki ta yankin Hong Kong karo na 7. Wannan shi ne zaben ’yan majalisar kafa dokoki ta yankin karo na farko, tun bayan aiwatar da manufar “tabbatar da ’yan kishin kasa su yi mulkin yankin Hong Kong”, da kuma sake fasalin tsarin majalisar kafa dokokin yankin.

Masharhanta na ganin cewa, yankin Hong Kong ya dauki kwakkwaran mataki, na tafiyar da harkokin yanki yadda ya kamata. Yanzu haka dai, an zabi mambobin kwamitocin gundumomin mazabu 176, da kuma kansilolin mazabu 88, matakin dake kara tabbatar da muhimmancin dokar tsaron kasa da aka kafa a yankin.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

Kuma tun lokacin da aka kafa, tare da fara aiwatar da dokar tsaron kasa mai nasaba da yankin Hong Kong, wadda wata muhimmiyar dama ce ta yanke hukunci ga baragurbin dake neman ta da rikici a yankin, lamarin da ya tabbatar da ci gaba mai dorewa a yankin, da ma tafiyar da tsarin nan na kasa daya amma tsarin mulki iri biyu yadda ya kamata.

Jagororin yankin dai sun sha nanata cewa, masu bin doka suna maraba da dokar tsaron da aka kafa, matakin da ya kara janyo masu sha’awar zuba da neman halaliya tare da kara dawo da martabar yankin a idon duniya.

Yanzu dai yankin Hong Kong ya zabi ’yan majalisu masu kishin kasa, wadanda za su kara janyowa yankin martaba da wadata. Matakin da masu sharhi ke cewa, ya bude wani sabon babi a yankin, tun bayan da aka kafa sabbin dokokin tsaron kasa da na zabe masu alaka da yankin. (Ibrahim Yaya)

Hong Kong
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

MASU ALAKA

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai
Daga Birnin Sin

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

July 20, 2026
Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare
Daga Birnin Sin

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso
Daga Birnin Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
Next Post
Ta Hanyar Hadin Gwiwa Ce Ake Iya Farfado Da Tattalin Arziki

Ta Hanyar Hadin Gwiwa Ce Ake Iya Farfado Da Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

July 20, 2026
Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

July 20, 2026
Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

July 20, 2026
Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026
Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

July 19, 2026
Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.