ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, September 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dokar Tsaron Kasa Ta Yi Kyakkyawan Tasiri A Yankin Hong Kong

by CGTN Hausa
3 years ago
Hong Kong

Sanin kowa ne cewa, kiyaye tsaron kasa, batu ne da ya shafi muhimman muradun kowace kasa a duniya. Kuma tun bayan da yankin musamman na Hong Kong ya dawo karkashin ikon kasar Sin, bisa ka’ida ta 23 cikin babbar dokar yankin, gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta dankawa yankin izinin kafa dokarsa ta fannin kiyaye tsaron kasa.

Sai dai kafin kafa dokar, yankin ya fuskanci wasu ayyuka na rashin doka a bangaren tsaron kasa wanda masana ke cewa, ba ya rasa nasaba da tsoma baki a harkokin yankin daga ketare.

Idan ba a manta ba a shekarar 2019, wasu bata-gari suka yi yunkurin balle Hong Kong daga kasar Sin, da cin zarafi gami da lalata tambari da tutar kasa, da zuga al’umma don su mamaye ofishin gwamnatin tsakiya dake Hong Kong, da kai hari kan mai uwa da wabi, da cin zarafin ’yan sanda wadanda a kullum suke sadaukar da rayukansu don tabbatar da tsaron al’umma, al’amuran da suka kasance ayyukan ta’addanci, da haifar da babbar barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a Hong Kong gami da cikakken iko na kasa.

ADVERTISEMENT

Kuma duk wata kasa da ta san abin da take yi, ba za ta amince da irin wannan danyen aiki ba. Bayan kafa wannan doka, a makon nan aka yi nasarar gudanar da zaben ’yan majalisar kafa dokoki ta yankin Hong Kong karo na 7. Wannan shi ne zaben ’yan majalisar kafa dokoki ta yankin karo na farko, tun bayan aiwatar da manufar “tabbatar da ’yan kishin kasa su yi mulkin yankin Hong Kong”, da kuma sake fasalin tsarin majalisar kafa dokokin yankin.

Masharhanta na ganin cewa, yankin Hong Kong ya dauki kwakkwaran mataki, na tafiyar da harkokin yanki yadda ya kamata. Yanzu haka dai, an zabi mambobin kwamitocin gundumomin mazabu 176, da kuma kansilolin mazabu 88, matakin dake kara tabbatar da muhimmancin dokar tsaron kasa da aka kafa a yankin.

LABARAI MASU NASABA

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Kuma tun lokacin da aka kafa, tare da fara aiwatar da dokar tsaron kasa mai nasaba da yankin Hong Kong, wadda wata muhimmiyar dama ce ta yanke hukunci ga baragurbin dake neman ta da rikici a yankin, lamarin da ya tabbatar da ci gaba mai dorewa a yankin, da ma tafiyar da tsarin nan na kasa daya amma tsarin mulki iri biyu yadda ya kamata.

Jagororin yankin dai sun sha nanata cewa, masu bin doka suna maraba da dokar tsaron da aka kafa, matakin da ya kara janyo masu sha’awar zuba da neman halaliya tare da kara dawo da martabar yankin a idon duniya.

Yanzu dai yankin Hong Kong ya zabi ’yan majalisu masu kishin kasa, wadanda za su kara janyowa yankin martaba da wadata. Matakin da masu sharhi ke cewa, ya bude wani sabon babi a yankin, tun bayan da aka kafa sabbin dokokin tsaron kasa da na zabe masu alaka da yankin. (Ibrahim Yaya)

Hong Kong
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Gabatar Da Shawarwari Kan Hadin Gwiwar “Gawurtacciyar Kungiyar BRICS”

MASU ALAKA

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi
Daga Birnin Sin

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

September 14, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi
Daga Birnin Sin

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin
Daga Birnin Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Next Post
Ta Hanyar Hadin Gwiwa Ce Ake Iya Farfado Da Tattalin Arziki

Ta Hanyar Hadin Gwiwa Ce Ake Iya Farfado Da Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Ta’aziyyar Bamanga: Gwamna Fintiri Ya Ayyana Litinin Ranar Hutun Aiki

Ta’aziyyar Bamanga: Gwamna Fintiri Ya Ayyana Litinin Ranar Hutun Aiki

September 14, 2026
Dangote

Matatar Dangote Ta Fara Sayar Da Hannun Jari Na Naira Tiriliyan 2.15

September 14, 2026
Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

September 14, 2026
CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

September 14, 2026
Dansanda Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 1 Kan Ya Saki Wani Barawon Mutane A Kano

Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 

September 14, 2026
Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Hong Kong

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.