ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Bukatar Kasar Sin Fiye Da Kowane Lokaci

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

Wasu nazarce-nazarce da jaridar Politico da kamfanin tsara nazarin ra’ayin jama’a na Public First suka gudanar a baya bayan nan sun gano cewa, mutane a kasashe 4 dake zaman manyan kawayen Amurka wato Canada da Jamus da Faransa da Birtaniya, suna ganin Sin a matsayin abar dogaro, wadda za ta iya taka ingantacciyar rawa a karni na 21.

Ba a wadannan kasashe ba kadai, farin jinin kasar Sin yana ta karuwa a duniya tsakanin kasashe daban-daban musamman a nahiyar Afrika da kudu maso gabashin Asia da sassan Latin Amurka da sauransu.

To ko mene ne dalili?

ADVERTISEMENT

Kai ya waye, ido ya bude, kowace kasa na son ta ga ta ci gaba, ta samu habakar tattalin arziki kuma ta tsaya da kafarta. Kuma wannan ita ce sabuwar dabarar da Sin ta bullo da ita a hadin gwiwar kasa da kasa, watau cin moriyar juna, hadin gwiwa cikin adalci da girmama juna ba tare da sharudda ko tsoma baki cikin harkokin wasu ba, sabanin yadda aka saba gani da ma yadda har yanzu wasu ’yan tsiraru ke neman danne tasowar kasashe da yin fatali da dokokin kasa da kasa da amfani da karfi domin wadata kansu.

A lokacin da ake bukatar hadin gwiwa da taimakekeniya tsakanin kasa da kasa, kasar Sin ta kara bude kofarta, tana kira ga kasashe su shigo su ci gajiyar ci gaban da ta samu da babbar kasuwar dake gare ta. Kowa yana son sauki, kuma kasar Sin ta gabatar da hakan ga kasashen duniya maimakon yadda wasu ke kara tsananta kulle kofa da tsaurara matakan cinikayya.

LABARAI MASU NASABA

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Idan ana magana ta ci gaba, to kowa ya san kasar Sin ta yi gaba sosai. Misali abubuwan da yanzu duniya ke mayar da hankali kan su, kamar kirkire-kirkiren fasahohin zamani da ayyukan masana’antu da makamashi mai tsafa da sauransu, duk kasar Sin ce jagora a wadannan bangare. Kuma ta sha fadi cewa, ci gabanta ba zai taba zama barazana ba, sai dai ya zama dama ga sauran kasashe. Kuma hakan ne tun da dimbin kasashe sun ci kuma suna kan cin gajiyar ci gaban kasar Sin. Wannan dalili ne ya sa shugabannin Turai suka yi ta kawo ziyara kasar Sin domin yanzu kowa ya san cewa, babu wanda zai iya dogaro da kansa shi kadai wajen samun ci gaba, haka kuma, duniya na bukatar kasar Sin.

Idan kuma muka yi la’akari da rikice-rikicen da suka addabi duniya, za mu ga cewa, Sin tana adawa da su. Kuma har kullum, burinta shi ne warware rikice-rikice ta hanyar lumana, kana a girma ’yancin dukkan kasashe ba tare da la’akari da girmansu ba.

Wadannan dalilai kalilan, na daga cikin irinsu masu tarin yawa da suka yi daidai da burin kasa da kasa da al’ummominsu a zamanin da muke ciki, kuma su suka sa kima da daraja da farin jinin Sin ke karuwa a idanun duniya, domin tana da karfin tabbatar da burin kasa da kasa na samun zaman lafiya da ci gaba na bai daya a duniya. (Faeza Mustapha)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
Daga Birnin Sin

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
Next Post
Xi: Ya Kamata A Kara Ingancin Zamanantarwa Irin Ta Sin Ta Hanyar Dashen Bishiyoyi

Xi: Ya Kamata A Kara Ingancin Zamanantarwa Irin Ta Sin Ta Hanyar Dashen Bishiyoyi

LABARAI MASU NASABA

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.