Jami’an Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) sun kama tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman.
An kama Mamman, wanda ya ɓuya bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 75 a gidan yari, a yankin Rigasa da ke Jihar Kaduna.
Shugaban EFCC, Ola Olukoyede, ne ya bayyana hakan ga manema labarai yayin wani taron manema labarai da ya gudana a hedikwatar hukumar.
Ya ce an kama tsohon ministan ne da misalin ƙarfe 3:30 na asubahin ranar.
In ba a manta ba, mun rahoto muku yadda Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja karkashin jagorancin Mai shari’a James Omotosho, ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75 a gidan yari bayan samun sa da laifin karkatarwa da halasta kuɗaɗen da aka ware domin aikin wutar lantarki da suka kai naira biliyan 33.8 a makon da ya gabata.
A yayin yanke hukuncin, Lauyan dake kare Ministan ya ce, bai san inda wanda yake karewa yake ba, inda ya ce, duk kokarin samunsa ta wayar salularsa ya ci tura.















Discussion about this post