ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Eid-el-Fitr: Gwamna Lawal Ya Buƙaci Musulmi Su Ƙara Addu’o’in Zaman Lafiya

by Sulaiman
6 months ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su ƙara himma wajen yin addu’o’i domin tabbatar da zaman lafiya a jihar Zamfara da kuma ƙasa baki ɗaya.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake taya Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan na kwanaki 30, tare da shiga bukukuwan Sallah Ƙaramar (Eid-el-Fitr), wadda ke nuna ƙarshen watan ibada da tsarkakewar ruhi.

ADVERTISEMENT
  • FIFA Ta Ci Tarar Nijeriya Da Congo
  • Yadda Shigo Da Shinkafa Daga Kasashen Waje Ya Share Masana’antu 90 A Nijeriya

A cikin saƙonsa na barka, Gwamna Lawal ya jaddada muhimmancin wannan lokaci na Sallah, yana mai cewa lokaci ne na farin ciki, godiya ga Allah, haɗin kai da kuma sabunta niyya.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Ya ƙara da cewa wannan lokaci na bukukuwa ya kamata ya zama wata dama ta ƙara tashi tsaye wajen neman zaman lafiya da haɗin kan al’umma.

 

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Musulmi a Zamfara da Nujeriya murnar kammala azumin watan Ramadan na kwanaki 30, tare da shiga bikin Eid-el-Fitr, wato ranar buɗe baki. Wannan lokaci ne na farin ciki da godiya, kuma ya kamata mu ƙara dagewa da addu’o’i domin zaman lafiya a jiharmu da ƙasarmu,” inji shi.

 

Gwamnan ya bayyana cewa azumin Ramadan da aka kammala yana da muhimmiyar rawa wajen koyar da haƙuri, ladabi, tausayi ga juna da kuma kusantar Allah, yana mai cewa waɗannan darussa su ne ginshiƙan gina al’umma mai nagarta.

 

Ya kuma jaddada cewa domin a samu ci gaba mai ɗorewa a Zamfara da Nijeriya, wajibi ne al’umma su haɗa kai, su rungumi juna tare da ɗaukar nauyin kula da juna, domin samar da makoma mai kyau ga kowa.

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya yi addu’ar Allah Ya sa a gudanar da bukukuwan Sallah cikin lumana da kwanciyar hankali, tare da fatan samun ƙoshin lafiya, zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki a shekaru masu zuwa.

 

SALLAH ƘARAMA: Gwamna Lawal Ya Buƙaci Musulmi Su Ƙara Addu’o’in Zaman Lafiya

 

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su ƙara himma wajen yin addu’o’i domin tabbatar da zaman lafiya a jihar Zamfara da kuma ƙasa baki ɗaya.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake taya Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan na kwanaki 30, tare da shiga bukukuwan Sallah Ƙaramar (Eid-el-Fitr), wadda ke nuna ƙarshen watan ibada da tsarkakewar ruhi.

 

A cikin saƙonsa na barka, Gwamna Lawal ya jaddada muhimmancin wannan lokaci na Sallah, yana mai cewa lokaci ne na farin ciki, godiya ga Allah, haɗin kai da kuma sabunta niyya.

 

Ya ƙara da cewa wannan lokaci na bukukuwa ya kamata ya zama wata dama ta ƙara tashi tsaye wajen neman zaman lafiya da haɗin kan al’umma.

 

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Musulmi a Zamfara da Nujeriya murnar kammala azumin watan Ramadan na kwanaki 30, tare da shiga bikin Eid-el-Fitr, wato ranar buɗe baki. Wannan lokaci ne na farin ciki da godiya, kuma ya kamata mu ƙara dagewa da addu’o’i domin zaman lafiya a jiharmu da ƙasarmu,” inji shi.

 

Gwamnan ya bayyana cewa azumin Ramadan da aka kammala yana da muhimmiyar rawa wajen koyar da haƙuri, ladabi, tausayi ga juna da kuma kusantar Allah, yana mai cewa waɗannan darussa su ne ginshiƙan gina al’umma mai nagarta.

 

Ya kuma jaddada cewa domin a samu ci gaba mai ɗorewa a Zamfara da Nijeriya, wajibi ne al’umma su haɗa kai, su rungumi juna tare da ɗaukar nauyin kula da juna, domin samar da makoma mai kyau ga kowa.

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya yi addu’ar Allah Ya sa a gudanar da bukukuwan Sallah cikin lumana da kwanciyar hankali, tare da fatan samun ƙoshin lafiya, zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki a shekaru masu zuwa.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
  • Sulaiman
    Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Lawal
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Next Post
Makusanci Ya Yi Garkuwa Da Ɗan Shekara 4 Tare Da Masa Kisan Gilla A Bauchi Bayan Amsar Kuɗin Fansa

Makusanci Ya Yi Garkuwa Da Ɗan Shekara 4 Tare Da Masa Kisan Gilla A Bauchi Bayan Amsar Kuɗin Fansa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Lawal

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Lawal

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.