ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Eid-el-Fitr: Gwamna Lawal Ya Buƙaci Musulmi Su Ƙara Addu’o’in Zaman Lafiya

by Sulaiman
2 months ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su ƙara himma wajen yin addu’o’i domin tabbatar da zaman lafiya a jihar Zamfara da kuma ƙasa baki ɗaya.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake taya Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan na kwanaki 30, tare da shiga bukukuwan Sallah Ƙaramar (Eid-el-Fitr), wadda ke nuna ƙarshen watan ibada da tsarkakewar ruhi.

ADVERTISEMENT
  • FIFA Ta Ci Tarar Nijeriya Da Congo
  • Yadda Shigo Da Shinkafa Daga Kasashen Waje Ya Share Masana’antu 90 A Nijeriya

A cikin saƙonsa na barka, Gwamna Lawal ya jaddada muhimmancin wannan lokaci na Sallah, yana mai cewa lokaci ne na farin ciki, godiya ga Allah, haɗin kai da kuma sabunta niyya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Ya ƙara da cewa wannan lokaci na bukukuwa ya kamata ya zama wata dama ta ƙara tashi tsaye wajen neman zaman lafiya da haɗin kan al’umma.

 

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Musulmi a Zamfara da Nujeriya murnar kammala azumin watan Ramadan na kwanaki 30, tare da shiga bikin Eid-el-Fitr, wato ranar buɗe baki. Wannan lokaci ne na farin ciki da godiya, kuma ya kamata mu ƙara dagewa da addu’o’i domin zaman lafiya a jiharmu da ƙasarmu,” inji shi.

 

Gwamnan ya bayyana cewa azumin Ramadan da aka kammala yana da muhimmiyar rawa wajen koyar da haƙuri, ladabi, tausayi ga juna da kuma kusantar Allah, yana mai cewa waɗannan darussa su ne ginshiƙan gina al’umma mai nagarta.

 

Ya kuma jaddada cewa domin a samu ci gaba mai ɗorewa a Zamfara da Nijeriya, wajibi ne al’umma su haɗa kai, su rungumi juna tare da ɗaukar nauyin kula da juna, domin samar da makoma mai kyau ga kowa.

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya yi addu’ar Allah Ya sa a gudanar da bukukuwan Sallah cikin lumana da kwanciyar hankali, tare da fatan samun ƙoshin lafiya, zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki a shekaru masu zuwa.

 

SALLAH ƘARAMA: Gwamna Lawal Ya Buƙaci Musulmi Su Ƙara Addu’o’in Zaman Lafiya

 

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su ƙara himma wajen yin addu’o’i domin tabbatar da zaman lafiya a jihar Zamfara da kuma ƙasa baki ɗaya.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake taya Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan na kwanaki 30, tare da shiga bukukuwan Sallah Ƙaramar (Eid-el-Fitr), wadda ke nuna ƙarshen watan ibada da tsarkakewar ruhi.

 

A cikin saƙonsa na barka, Gwamna Lawal ya jaddada muhimmancin wannan lokaci na Sallah, yana mai cewa lokaci ne na farin ciki, godiya ga Allah, haɗin kai da kuma sabunta niyya.

 

Ya ƙara da cewa wannan lokaci na bukukuwa ya kamata ya zama wata dama ta ƙara tashi tsaye wajen neman zaman lafiya da haɗin kan al’umma.

 

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Musulmi a Zamfara da Nujeriya murnar kammala azumin watan Ramadan na kwanaki 30, tare da shiga bikin Eid-el-Fitr, wato ranar buɗe baki. Wannan lokaci ne na farin ciki da godiya, kuma ya kamata mu ƙara dagewa da addu’o’i domin zaman lafiya a jiharmu da ƙasarmu,” inji shi.

 

Gwamnan ya bayyana cewa azumin Ramadan da aka kammala yana da muhimmiyar rawa wajen koyar da haƙuri, ladabi, tausayi ga juna da kuma kusantar Allah, yana mai cewa waɗannan darussa su ne ginshiƙan gina al’umma mai nagarta.

 

Ya kuma jaddada cewa domin a samu ci gaba mai ɗorewa a Zamfara da Nijeriya, wajibi ne al’umma su haɗa kai, su rungumi juna tare da ɗaukar nauyin kula da juna, domin samar da makoma mai kyau ga kowa.

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya yi addu’ar Allah Ya sa a gudanar da bukukuwan Sallah cikin lumana da kwanciyar hankali, tare da fatan samun ƙoshin lafiya, zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki a shekaru masu zuwa.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Makusanci Ya Yi Garkuwa Da Ɗan Shekara 4 Tare Da Masa Kisan Gilla A Bauchi Bayan Amsar Kuɗin Fansa

Makusanci Ya Yi Garkuwa Da Ɗan Shekara 4 Tare Da Masa Kisan Gilla A Bauchi Bayan Amsar Kuɗin Fansa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.