ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makusanci Ya Yi Garkuwa Da Ɗan Shekara 4 Tare Da Masa Kisan Gilla A Bauchi Bayan Amsar Kuɗin Fansa

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 months ago
Bauchi

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta kama wani matashi ɗan shekara 20 mai suna Rabiu Safiyanu, bisa zarginsa da yin garkuwa da kashe wani ƙaramin yaro ɗan shekara 4 a duniya mai suna Yunusa Salisu.

 

Mahaifin yaron Malam Salisu Yunusa, mazaunin unguwar Nasarawa Madina Quarters a cikin garin Bauchi ne ya kai rahoton ɓacewar ɗan nasa ga ‘yansanda a ranar 21 ga Maris. Ya ce sun nemi yaron nasu tun ranar 18 ga watan Maris sun rasa.

ADVERTISEMENT
  • Burina Na Gaba Bayan Fim Shi Ne Aure —Khadija
  • Harin Bam A Maiduguri: Har Yanzu Akwai ’Yan Ƙunar Baƙin Wake Biyu Da Suka Yi Ɓatan Dabo – Zulum 

A cewar mahaifin, su na wannan halin kuma sai ya samu ƙiran waya a ranar 19 ga Maris daga wani mutum ta wata lamba a ɓoye, inda aka buƙaci ya biya kuɗin fansa na N500,000. Ya ce ya biya N100,000 domin ganin an saki ɗansa, amma duk da biyan kuɗin ba a sako ɗan nasa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Bauchi (PPRO), SP Nafiu Habib, ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana cewa jami’an bincike daga caji ofis ɗin ‘C’ Division, ƙarƙashin jagorancin babban Baturen ɗansanda (DPO), sun fara bincike bayan samun rahoton.

 

Binciken ya kai ga kama Rabiu Safiyanu, mai shekaru 20, wanda ke zaune a addreshi guda da mahaifin yaron, kuma aboki ne ga ƙanin mai koken ɓacewar ɗansa. Kasancewarsa abokin ƙanin mahaifin yaron ya ba shi damar shiga gidan a duk lokacin da ya ke so cikin sauƙi.

 

‘Yansanda sun ce wanda ake zargin ya amsa laifin ɗaukar yaron, ya shake shi, ya jefar da gawar a tsaunukan Warinje, sannan ya nemi ƙarin kuɗin fansa, bayan wanda ya amsa daga fari.

 

Daga bisani, ‘yansanda sun gano gawar yaron wadda ta fara ruɓewa, tare da alamun an shaƙe shi. Haka kuma an samu igiya da ake zargin an yi amfani da ita wajen aikata wannan ɗanyen aikin.

 

Jami’in da ke kula da asibitin ‘yansanda ya tabbatar da mutuwar yaron. An ɗauki hotunan gawar kafin daga bisani a miƙa ta ga iyalansa, inda aka binne ta nan take saboda dalilan kiyaye lafiyar jama’a.

 

SP Nafiu Habib ya ƙara da cewa wanda ake zargin yana hannun ‘yansanda domin ci gaba da bincike.

 

Kwamishinan ‘yansandan Jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umarci sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) da ya karɓi kes ɗin domin tabbatar da cikakken bincike cikin gaggawa da kuma gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu.

 

Ya kuma buƙaci al’umma da su kasance masu lura tare da kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba ga ‘yansanda domin samun damar daukan matakan gaggawa a duk lokacin buƙatar hakan.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Eid-el-Fitr: Shettima Ya Jaddada Muhimmancin Zaman Lafiya da Ci Gaba a Nijeriya

Eid-el-Fitr: Shettima Ya Jaddada Muhimmancin Zaman Lafiya da Ci Gaba a Nijeriya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.