ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makusanci Ya Yi Garkuwa Da Ɗan Shekara 4 Tare Da Masa Kisan Gilla A Bauchi Bayan Amsar Kuɗin Fansa

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Bauchi

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta kama wani matashi ɗan shekara 20 mai suna Rabiu Safiyanu, bisa zarginsa da yin garkuwa da kashe wani ƙaramin yaro ɗan shekara 4 a duniya mai suna Yunusa Salisu.

 

Mahaifin yaron Malam Salisu Yunusa, mazaunin unguwar Nasarawa Madina Quarters a cikin garin Bauchi ne ya kai rahoton ɓacewar ɗan nasa ga ‘yansanda a ranar 21 ga Maris. Ya ce sun nemi yaron nasu tun ranar 18 ga watan Maris sun rasa.

ADVERTISEMENT
  • Burina Na Gaba Bayan Fim Shi Ne Aure —Khadija
  • Harin Bam A Maiduguri: Har Yanzu Akwai ’Yan Ƙunar Baƙin Wake Biyu Da Suka Yi Ɓatan Dabo – Zulum 

A cewar mahaifin, su na wannan halin kuma sai ya samu ƙiran waya a ranar 19 ga Maris daga wani mutum ta wata lamba a ɓoye, inda aka buƙaci ya biya kuɗin fansa na N500,000. Ya ce ya biya N100,000 domin ganin an saki ɗansa, amma duk da biyan kuɗin ba a sako ɗan nasa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Bauchi (PPRO), SP Nafiu Habib, ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana cewa jami’an bincike daga caji ofis ɗin ‘C’ Division, ƙarƙashin jagorancin babban Baturen ɗansanda (DPO), sun fara bincike bayan samun rahoton.

 

Binciken ya kai ga kama Rabiu Safiyanu, mai shekaru 20, wanda ke zaune a addreshi guda da mahaifin yaron, kuma aboki ne ga ƙanin mai koken ɓacewar ɗansa. Kasancewarsa abokin ƙanin mahaifin yaron ya ba shi damar shiga gidan a duk lokacin da ya ke so cikin sauƙi.

 

‘Yansanda sun ce wanda ake zargin ya amsa laifin ɗaukar yaron, ya shake shi, ya jefar da gawar a tsaunukan Warinje, sannan ya nemi ƙarin kuɗin fansa, bayan wanda ya amsa daga fari.

 

Daga bisani, ‘yansanda sun gano gawar yaron wadda ta fara ruɓewa, tare da alamun an shaƙe shi. Haka kuma an samu igiya da ake zargin an yi amfani da ita wajen aikata wannan ɗanyen aikin.

 

Jami’in da ke kula da asibitin ‘yansanda ya tabbatar da mutuwar yaron. An ɗauki hotunan gawar kafin daga bisani a miƙa ta ga iyalansa, inda aka binne ta nan take saboda dalilan kiyaye lafiyar jama’a.

 

SP Nafiu Habib ya ƙara da cewa wanda ake zargin yana hannun ‘yansanda domin ci gaba da bincike.

 

Kwamishinan ‘yansandan Jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umarci sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) da ya karɓi kes ɗin domin tabbatar da cikakken bincike cikin gaggawa da kuma gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu.

 

Ya kuma buƙaci al’umma da su kasance masu lura tare da kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba ga ‘yansanda domin samun damar daukan matakan gaggawa a duk lokacin buƙatar hakan.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Eid-el-Fitr: Shettima Ya Jaddada Muhimmancin Zaman Lafiya da Ci Gaba a Nijeriya

Eid-el-Fitr: Shettima Ya Jaddada Muhimmancin Zaman Lafiya da Ci Gaba a Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.