ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makusanci Ya Yi Garkuwa Da Ɗan Shekara 4 Tare Da Masa Kisan Gilla A Bauchi Bayan Amsar Kuɗin Fansa

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 months ago
Bauchi

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta kama wani matashi ɗan shekara 20 mai suna Rabiu Safiyanu, bisa zarginsa da yin garkuwa da kashe wani ƙaramin yaro ɗan shekara 4 a duniya mai suna Yunusa Salisu.

 

Mahaifin yaron Malam Salisu Yunusa, mazaunin unguwar Nasarawa Madina Quarters a cikin garin Bauchi ne ya kai rahoton ɓacewar ɗan nasa ga ‘yansanda a ranar 21 ga Maris. Ya ce sun nemi yaron nasu tun ranar 18 ga watan Maris sun rasa.

ADVERTISEMENT
  • Burina Na Gaba Bayan Fim Shi Ne Aure —Khadija
  • Harin Bam A Maiduguri: Har Yanzu Akwai ’Yan Ƙunar Baƙin Wake Biyu Da Suka Yi Ɓatan Dabo – Zulum 

A cewar mahaifin, su na wannan halin kuma sai ya samu ƙiran waya a ranar 19 ga Maris daga wani mutum ta wata lamba a ɓoye, inda aka buƙaci ya biya kuɗin fansa na N500,000. Ya ce ya biya N100,000 domin ganin an saki ɗansa, amma duk da biyan kuɗin ba a sako ɗan nasa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Bauchi (PPRO), SP Nafiu Habib, ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana cewa jami’an bincike daga caji ofis ɗin ‘C’ Division, ƙarƙashin jagorancin babban Baturen ɗansanda (DPO), sun fara bincike bayan samun rahoton.

 

Binciken ya kai ga kama Rabiu Safiyanu, mai shekaru 20, wanda ke zaune a addreshi guda da mahaifin yaron, kuma aboki ne ga ƙanin mai koken ɓacewar ɗansa. Kasancewarsa abokin ƙanin mahaifin yaron ya ba shi damar shiga gidan a duk lokacin da ya ke so cikin sauƙi.

 

‘Yansanda sun ce wanda ake zargin ya amsa laifin ɗaukar yaron, ya shake shi, ya jefar da gawar a tsaunukan Warinje, sannan ya nemi ƙarin kuɗin fansa, bayan wanda ya amsa daga fari.

 

Daga bisani, ‘yansanda sun gano gawar yaron wadda ta fara ruɓewa, tare da alamun an shaƙe shi. Haka kuma an samu igiya da ake zargin an yi amfani da ita wajen aikata wannan ɗanyen aikin.

 

Jami’in da ke kula da asibitin ‘yansanda ya tabbatar da mutuwar yaron. An ɗauki hotunan gawar kafin daga bisani a miƙa ta ga iyalansa, inda aka binne ta nan take saboda dalilan kiyaye lafiyar jama’a.

 

SP Nafiu Habib ya ƙara da cewa wanda ake zargin yana hannun ‘yansanda domin ci gaba da bincike.

 

Kwamishinan ‘yansandan Jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umarci sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) da ya karɓi kes ɗin domin tabbatar da cikakken bincike cikin gaggawa da kuma gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu.

 

Ya kuma buƙaci al’umma da su kasance masu lura tare da kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba ga ‘yansanda domin samun damar daukan matakan gaggawa a duk lokacin buƙatar hakan.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Eid-el-Fitr: Shettima Ya Jaddada Muhimmancin Zaman Lafiya da Ci Gaba a Nijeriya

Eid-el-Fitr: Shettima Ya Jaddada Muhimmancin Zaman Lafiya da Ci Gaba a Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.