Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya sake nuna kudirinsa na sauya fasalin tattalin arziki da ci gaban jihar bayan sanya hannu kan wasu muhimman dokoki guda uku da ake sa ran za su kawo gagarumin sauyi a fannin wutar lantarki, noma da kuma kare muhalli.
Dokokin da gwamnan ya amince da su sun hada da Dokar Wutar Lantarki ta Jihar Kaduna ta 2026 da dokar asusun bunƙasa noma ta Kaduna (KADFund) ta 2025, da kuma dokar hukumar ba da Shawara Kan Sauyin Yanayi ta Jihar Kaduna ta 2026.
A wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ya fitar, ya bayyana cewa sabbin dokokin za su samar da ingantaccen tsari da zai taimaka wajen jawo masu zuba jari, ƙarfafa samar da abinci, da kuma magance kalubalen sauyin yanayi.
Maiyaki ya ce dokar wutar lantarki za ta bai wa jihar damar tsara da kula da harkokin samarwa da rarraba wutar lantarki, tare da bude kofar zuba jari ga kamfanoni masu zaman kansu da bunkasa amfani da makamashi mai sabuntawa.
Haka kuma, ya ce dokar KADFund ta samar da wani asusu na musamman da zai tallafa wa manoma, kungiyoyin hadin gwiwa da masu harkokin kasuwancin noma ta hanyar ba su tallafi, rance mai sauki da kuma samar da muhimman ababen more rayuwa.
Gwamnatin jihar ta ce wadannan dokoki sun kara tabbatar da kudirin Gwamna Uba Sani na gina Kaduna mai ci gaba, wadda za ta kasance abar koyi a fannin zuba jari, samar da abinci da kuma kare muhalli a Nijeriya.















Discussion about this post