A wani ci gaban kuma hukumar kwallon kafa ta FIFA ce ta ci tarar Nijeriya bayan da kwamitin ladabtarwa na hukumar ya samu Nijeriya da laifin kin dokokin jami’an tsaro a filin wasa ta hanyar jifa da magoya bayan Super Eagles din suka yi a lokacin wasa tsakanin Nijeriya da Kasar ta Congo a watan Nuwamba. FIFA ta ce Nijeriya ta karya doka karkashin sashi na 17 da sashi na 12 biyu cikin baka na dokokin hukumar kuma an ci tarar Nijeriya Swiss franc 1,000.
Ita ma Congo, FIFA ta ci tararta Swiss franc dubu biyar bias samun magoya bayan kasar da yin amfani da fitila wajen haske fuskar ‘yanwasan Nijeriya, laifin nasu kuma ya saba wa kundin hukumar FIFA, sashe na 17 biyu cikin baka. Idan mai karatu bai manta ba, bayan tashi daga wasan ne kociyan tawagar Nijeriya, Eric Chelle ya zargi Congo da yin amfani da tsafi a wasan da Nijeriya ta yi rashin nasara a bugun daga kai sai mai tsaron raga a wasan da aka fafata a kasar Moroko.















Discussion about this post