Fadar Shugaban Ƙasa ta yi watsi da kiran da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi na neman Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi murabus.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar, fadar shugaban ƙasa ta ce kalaman Obi ba su fayyace gaskiyar halin da Nijeriya ke ciki ba.
Sanarwar ta bayyana cewa Nijeriya na amfani da tsarin shugabanci na shugaban ƙasa ne, ba irin na majalisar dokoki kamar na Birtaniya ba, don haka shugaban ƙasa yana da wa’adin shekaru huɗu da doka ta tanada, kuma ba a sauke shi da kiran jama’a ko rubuce-rubuce a shafukan sada zumunta ba.
Ta kuma ce sakamakon zaɓe na baya-bayan nan ya nuna cewa Tinubu na da goyon bayan jama’a, inda ta ce ya kamata Obi ya jira lokacin zaɓen 2027 maimakon yin kiranye-kiranye a shafin X.
A ɓangaren tsaro, fadar shugaban ƙasa ta ce gwamnati ta samu nasarori wajen ceto waɗanda aka yi garkuwa da su, da kakkaɓe ‘yan ta’adda, da kuma ƙarfafa aikin sojoji a faɗin ƙasar.
Ta kuma ce an kawar da ‘yan ta’adda sama da 15,000 a dazuka, sannan an inganta kayan aiki da horar da jami’an tsaro a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.
A ɓangaren tattalin arziƙi, sanarwar ta ce Nijeriya na samun ci gaba ta hanyar haƙar mai, ƙarin kuɗaɗen shiga, da zuba jari daga ƙasashen waje.
Ta ƙara da cewa matsin tattalin arziƙi da hauhawar farashi matsala ce ta duniya baki ɗaya, ba ta Nijeriya kaɗai ba, tana danganta hakan da rikice-rikicen duniya.
A ƙarshe, fadar shugaban ƙasa ta bayyana kiran Obi a matsayin siyasa, tana mai cewa Shugaba Tinubu yana mayar da hankali kan gyare-gyare, tsaro, da bunkasa tattalin arziƙi.















Discussion about this post