ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

by Sadiq
1 hour ago

Fadar Shugaban Ƙasa ta yi watsi da kiran da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi na neman Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi murabus.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar, fadar shugaban ƙasa ta ce kalaman Obi ba su fayyace gaskiyar halin da Nijeriya ke ciki ba.

Sanarwar ta bayyana cewa Nijeriya na amfani da tsarin shugabanci na shugaban ƙasa ne, ba irin na majalisar dokoki kamar na Birtaniya ba, don haka shugaban ƙasa yana da wa’adin shekaru huɗu da doka ta tanada, kuma ba a sauke shi da kiran jama’a ko rubuce-rubuce a shafukan sada zumunta ba.

ADVERTISEMENT

Ta kuma ce sakamakon zaɓe na baya-bayan nan ya nuna cewa Tinubu na da goyon bayan jama’a, inda ta ce ya kamata Obi ya jira lokacin zaɓen 2027 maimakon yin kiranye-kiranye a shafin X.

A ɓangaren tsaro, fadar shugaban ƙasa ta ce gwamnati ta samu nasarori wajen ceto waɗanda aka yi garkuwa da su, da kakkaɓe ‘yan ta’adda, da kuma ƙarfafa aikin sojoji a faɗin ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutane 19 A Wani Sabon Hari A Filato

Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi

Ta kuma ce an kawar da ‘yan ta’adda sama da 15,000 a dazuka, sannan an inganta kayan aiki da horar da jami’an tsaro a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.

A ɓangaren tattalin arziƙi, sanarwar ta ce Nijeriya na samun ci gaba ta hanyar haƙar mai, ƙarin kuɗaɗen shiga, da zuba jari daga ƙasashen waje.

Ta ƙara da cewa matsin tattalin arziƙi da hauhawar farashi matsala ce ta duniya baki ɗaya, ba ta Nijeriya kaɗai ba, tana danganta hakan da rikice-rikicen duniya.

A ƙarshe, fadar shugaban ƙasa ta bayyana kiran Obi a matsayin siyasa, tana mai cewa Shugaba Tinubu yana mayar da hankali kan gyare-gyare, tsaro, da bunkasa tattalin arziƙi.

MASU ALAKA

’Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 28 A Jihar Filato
Manyan Labarai

An Kashe Mutane 19 A Wani Sabon Hari A Filato

June 23, 2026
Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi

June 23, 2026
Tinubu Ya Yi Murabus Saboda Ya Gaza A Kan Matsalar Tsaro – Peter Obi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Yi Murabus Saboda Ya Gaza A Kan Matsalar Tsaro – Peter Obi

June 23, 2026
Next Post
Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

June 23, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 47 Da ISWAP Suka Sace A Jihar Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 47 Da ISWAP Suka Sace A Jihar Borno

June 23, 2026
’Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 28 A Jihar Filato

An Kashe Mutane 19 A Wani Sabon Hari A Filato

June 23, 2026
Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi

Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi

June 23, 2026
Tinubu Ya Yi Murabus Saboda Ya Gaza A Kan Matsalar Tsaro – Peter Obi

Tinubu Ya Yi Murabus Saboda Ya Gaza A Kan Matsalar Tsaro – Peter Obi

June 23, 2026
An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

June 22, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jaddada Aniyarta Na Ƙin Sulhu Da ‘Yan Ta’adda

Gwamnatin Zamfara Ta Jaddada Aniyarta Na Ƙin Sulhu Da ‘Yan Ta’adda

June 22, 2026
Kudin Shigar Gwamnatin Sin Ya Karu Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Kudin Shigar Gwamnatin Sin Ya Karu Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 22, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.