Aƙalla yara 14 ne suka rasu yayin da wasu huɗu suka jikkata sakamakon wata gobara da ta tashi a wani bene mai hawa uku a birnin Lucknow na ƙasar Indiya a ranar Litinin.
Benen na ɗauke da ɗakin karatu, cibiyar koyar da ɗalibai da kuma sashen koyar da fasahar kwamfuta.
Gobarar ta fara ne daga hawa na tsakiya kafin ta bazu zuwa sauran sassan ginin.
Shaidu sun ce wasu ɗalibai sun yi ta tsalle daga saman bene domin tsira daga gobarar.
Bidiyo da hotuna sun nuna yadda jami’an kashe gobara ke ƙoƙarin shawo kan wutar da ta mamaye ginin.
Mataimakin Gwamnan Jihar Uttar Pradesh, Brajesh Pathak, ya tabbatar da mutuwar yaran tare da bayyana cewa za a hukunta duk wanda aka samu da laifi kan lamarin.
Har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba.
Irin wannan gobara na yawan faruwa a Indiya saboda rashin bin ja’idoji da kuma matsalolin wayoyin lantarki.
Firaministan Indiya, Narendra Modi, ya bayyana alhininsa kan lamarin tare da bayar da tallafin kuɗi ga iyalan waɗanda suka rasu.















Discussion about this post