• Leadership Hausa
Sunday, August 7, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Rahotonni

Gamayyar Matasan Arewa A Kudu Ta Yi Tir Da Karuwar Ta’addanci A Arewa

by Abdulrazaq Yahuza
2 months ago
in Rahotonni
0
Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa da ke Kudancin Nijeriya a Jihar Legas ta yi Allah wadai da yadda hare-haren ta’addanci suke kara tsamari a yankunan arewa.

Gamayyar wacce ta nuna takaicinta kan lamarin ta bakin shugabanta, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci, ta bayyana cewa bisa irin ukubar da ake sha, lokaci ya yi da mutanen arewa za su gane ba su da shugabanni masu kishin su, “domin yadda ake kashe mutane tsakanin Katsina, Sakkwato, Zamfara da Kaduna babu ji babu gani kuma an ja baki an yi shuru abin ya wuce hankali. Shin akwai maganar da wasu za su fada nan gaba mu ji su mu yi aiki da su kuwa?”
“Domin kamar tsuntsu ya fi Dan’adam daraja a Nijeriya musamman wanda ya fito daga yankin arewacin kasar, wato su a tunanin shugabaninmu ba mu san abin da muke yi ba ko? A sace mu a dinga yi mana kisan gilla amma ko a jikinsu muna kira da babbar murya ga masu madafan iko na arewacin kasar nan da su yi karatun ta nutsu saboda duk nisan jifa kasa za ta sauko.

  • Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

“Tun a 1999 ake yakar arewa ana sace dukiyar da Allah ya shimfida a yankin. A bisa wannan ne ma aka kirkiri boko haram da fadar Fulani makiyaya, ga ‘yan kungiyar aware ta kabilar ibo, ga kungiyoyin yarabawa. Duk wadannan kungiyoyin ba su da wani buri ban da kisan mutanen arewa.” In ji gamayyar.

Wakazalika gamayyar ta ce a halin yanzu abin ya zama wa ‘yan arewa gaba-kura-baya-siyaki saboda ana kashe a yankinsu, sannan yankunan da wasunsu suka fita neman abinci ma ana musu barazana, tana mai cewa, “Ba za mu manta da kalaman da Gwannan Ondo ya yi a kan jama’ar arewacin kasar nan wanda ya ce Hausa/Fulani tarihi yana maimaita kansa, su Sardauna, Tafawa Balewa da Murtala Ramat Muhammed duk kisan gilla aka yi musu, Kun manta da wannan? Dan hakka ku canja tunani saboda lokaci ya kusan kure muku.

Wai a ce daga bakin gwamna ne sukutum wannan maganar ta fito kuma babu mai nuna masa yatsa daga arewar, to ina ake so al’ummarmu ta saka kanta?”

Labarai Masu Nasaba

Mu Kula Da Wayoyin Da Ke Hannun Yara

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Fitar Da Gwani: Tsarin Daliget Ya Yi Kancal Ga Yawancin ‘Yan Majalisarmu —Gbajabiamila

Next Post

‘Yan Sanda Sun Ceto Matar Shugaban APC Na Jihar Neja Da Aka Sace A Borno

Related

Mu Kula Da Wayoyin Da Ke Hannun Yara
Rahotonni

Mu Kula Da Wayoyin Da Ke Hannun Yara

14 hours ago
Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto
Rahotonni

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

15 hours ago
Amfanin Manhajar XENDER A Wayoyin Hannu
Rahotonni

Amfanin Manhajar XENDER A Wayoyin Hannu

1 day ago
Yaje-Yajen Aiki Na Neman Yi Wa Gwamnatin Buhari Katutu 
Rahotonni

Yaje-Yajen Aiki Na Neman Yi Wa Gwamnatin Buhari Katutu 

2 days ago
Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya
Rahotonni

Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

2 days ago
NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69
Rahotonni

NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69

3 days ago
Next Post
An Yi Garkuwa Da Matar Shugaban APC Na Karamar Hukumar Magama A Jihar Neja

'Yan Sanda Sun Ceto Matar Shugaban APC Na Jihar Neja Da Aka Sace A Borno

LABARAI MASU NASABA

NIS Ta Cafke Dillalan Makamai A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NIS Ta Cafke Dillalan Makamai A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 7, 2022
Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

August 7, 2022
Peter Obi Ba Zaiyi Nasarar Lashe Koda Rabin Jihar Nasarawa Ba – Inji Deji Adeyanju

Peter Obi Ba Zaiyi Nasarar Lashe Koda Rabin Jihar Nasarawa Ba – Inji Deji Adeyanju

August 7, 2022
Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

August 7, 2022
MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

August 7, 2022
Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

August 7, 2022
Wakilin Sin Ya Ki Amincewa Da Zargin Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Makamashin Nukiliyar Kasar Sin

Wakilin Sin Ya Ki Amincewa Da Zargin Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Makamashin Nukiliyar Kasar Sin

August 7, 2022
NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

August 7, 2022
Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

August 7, 2022
Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

August 7, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.