• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A matsayinta na shugabar kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a wannan wata, kasar Sin, bisa jagorancin wakilinta na dindindin, ta kira taro kan samar da tsarin tsaro da ya dace da yanayin da ake ciki da girmama cikakken ’yanci da yankunan dukkan kasashe, domin samun yanayin tsaro mai karko a duniya. 

Hakika kiran wannan taron da Wakilin Sin Zhang Jun ya yi ta zo a daidai lokacin da ya dace, ganin yanayin kalubale da duniya take ciki da kuma yadda ake keta cikakken ’yancin kasashe da takalar fada da kuma ingiza tayar da rikici.

  • Sin Ta Bayyana Kalaman Jakadan Amurka A Sin A Matsayin Shaidar Dake Nuna Tunani Irin Na Danniya

Zamanin mulkin mallaka da danniya ko cinikin bayi ya wuce. Ana cikin wani sabon zamani da ake neman ci gaba ta hanyar girmamawa da moriyar juna.

Akwai bukatar kasashen da suke ganin su shafaffu da mai ne, su dai na kokarin dawo da hannun agogo baya, domin duniya ta ci gaba. Girmama cikakken ’yancin kasa ya zama wajibi a kan kowacce kasa babba, ko karama.

Kasashen duniya da al’ummominsu sun bambanta, suka san yanayin da suke ciki da manufofi mafi dacewa da su, kuma su kadai ne za su san yadda ya kamata su shawo kan matsalolin dake addabarsu.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Don haka, bai kamata a rika nunawa kasashe fin karfi kan harkokinsu na gida ba, ko kuma a rika nuna musu an fi su sanin abun da ya fi dacewa da su ba.

Kamar yadda Zhang Jun ya bayyana yayin taron, dole ne a samu bambancin ra’ayi daga kasa da kasa kan batutuwan tsaro, amma ya kamata a samu daidaito ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa.

Shirin tsaron duniya da shugaban kasar Sin ya gabatar ga taron BOAO a watan Afrilu, ya gabatar da wata alkibla ta cimma tsaro na bai daya tare da warware matsaloli masu masu ruwa da tsaki.

An riga an san kasar Sin ba mai kaunar rikici ba ce, domin an ji, kuma an ga yadda al’ummominta da suka kunshi kabilu daban daban ke rayuwa cikin jituwa da zaman lafiya, don haka duk wani shiri da za ta gabatar don gane da hakan, a ganina abu ne da ya kamata a karba da hannu bibbiyu, tun da burinta shi ne, gina duniya mai kyakkaywar makoma cike da tsaro da kwanciyar hankali.

Akwai bukatar sauran kasashen duniya su mara mata baya, kuma su ma su yunkura, su hada karfi da karfi wajen ganin an samu ci gaban duniya da kwanciyar hankali, ta hanyar hakuri da girmama juna da tabbatar da adalci. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyan Alkawari Cikawa

Next Post

Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

Related

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

13 hours ago
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600
Daga Birnin Sin

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

14 hours ago
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda
Daga Birnin Sin

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

15 hours ago
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”
Daga Birnin Sin

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

15 hours ago
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

17 hours ago
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

18 hours ago
Next Post
Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

May 30, 2025
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

May 30, 2025
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

May 30, 2025
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

May 30, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.