ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
7 months ago
Gobara

Ibtila’in gobara ta hallaka mutane biyu tare da lalata kadarorin da darajarta ta kai naira biliyan 1.59 a Jihar Bauchi tsakanin Janairu zuwa Disamba 2025, kamar yadda hukumar kashe gobara ta tarayya (FFS) ta bayyana.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar FFS ta jihar Bauchi, Umar Lawal, ne ya bayyana hakan a cikin rahoton kididdigar gobara da aka fitar ga ‘yan jarida a ranar Litinin a Bauchi.

  • Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Bunkasa A Shekarar 2025
  • Kudaden Bincike Da Samar Da Ci Gaba Na Kamfanonin Gwamnatin Sin Sun Ci Gaba Da Haura Yuan Tiriliyan Daya Cikin Shekaru Hudu A Jere

A cewarsa, hukumar ta amsa kiran gaggawa domin ta zo ta kashe gobara guda 167 a tsakanin wannan lokacin, inda aka ceto rayukan mutane hudu tare da kare kadarorin da darajarta ta kai Naira biliyan 2.86 daga lalacewa.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa gobarar ta shafi gine-ginen jama’a da na gwamnati, gidajen masu zaman kansu, cibiyoyin ilimi, kasuwanni, tashoshin man fetur da iskar gas, da kuma motoci a fadin jihar.

Yayin da ya ke yin bayani dalla-dalla, Lawal ya ce gobara guda 10 sun auku a gine-ginen jama’a da na gwamnati, inda aka yi asarar dukiya mai darajar Naira miliyan 23, yayin da aka ceto kadarori da darajarsu ta kai Naira miliyan 855.1.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ya kara da cewa an samu gobara guda 80 a gidajen masu zaman kansu, lamarin da ya janyo lalacewar dukiya na Naira miliyan 605, yayin da aka ceto dukiya ta kai Naira biliyan 1.4.

Ya kuma ce gobara a cibiyoyin ilimi ta lalata kadarorin Naira miliyan 120, yayin da aka ceto Naira miliyan 200, “An samu gobara guda biyar a kasuwanni, inda aka yi asarar kadarorin Naira miliyan 45, yayin da aka ceto Naira miliyan 90,” in ji shi.

Lawal ya kara da cewa gobara guda 15 sun shafi tashoshin man fetur da iskar gas, inda aka yi asarar Naira miliyan 23.7, yayin da aka ceto kadarorin Naira miliyan 53.

Ya ce kuma an samu wasu gobara guda 15 da suka shafi motoci, inda aka lalata dukiya mai darajar Naira miliyan 70, yayin da aka ceto Naira miliyan 33.

Mai magana da yawun FFS ya danganta yawancin gobarar da matsalar kayan lantarki, tashin wutar lantarki (power surge), adana man fetur ba bisa ka’ida ba da hatsarori.

Gobara
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Hana Al’ummar Cuba ‘Yancin Rayuwa Da Samun Ci Gaba

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Hana Al'ummar Cuba ‘Yancin Rayuwa Da Samun Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.