ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
5 months ago
Gobara

Ibtila’in gobara ta hallaka mutane biyu tare da lalata kadarorin da darajarta ta kai naira biliyan 1.59 a Jihar Bauchi tsakanin Janairu zuwa Disamba 2025, kamar yadda hukumar kashe gobara ta tarayya (FFS) ta bayyana.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar FFS ta jihar Bauchi, Umar Lawal, ne ya bayyana hakan a cikin rahoton kididdigar gobara da aka fitar ga ‘yan jarida a ranar Litinin a Bauchi.

  • Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Bunkasa A Shekarar 2025
  • Kudaden Bincike Da Samar Da Ci Gaba Na Kamfanonin Gwamnatin Sin Sun Ci Gaba Da Haura Yuan Tiriliyan Daya Cikin Shekaru Hudu A Jere

A cewarsa, hukumar ta amsa kiran gaggawa domin ta zo ta kashe gobara guda 167 a tsakanin wannan lokacin, inda aka ceto rayukan mutane hudu tare da kare kadarorin da darajarta ta kai Naira biliyan 2.86 daga lalacewa.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa gobarar ta shafi gine-ginen jama’a da na gwamnati, gidajen masu zaman kansu, cibiyoyin ilimi, kasuwanni, tashoshin man fetur da iskar gas, da kuma motoci a fadin jihar.

Yayin da ya ke yin bayani dalla-dalla, Lawal ya ce gobara guda 10 sun auku a gine-ginen jama’a da na gwamnati, inda aka yi asarar dukiya mai darajar Naira miliyan 23, yayin da aka ceto kadarori da darajarsu ta kai Naira miliyan 855.1.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ya kara da cewa an samu gobara guda 80 a gidajen masu zaman kansu, lamarin da ya janyo lalacewar dukiya na Naira miliyan 605, yayin da aka ceto dukiya ta kai Naira biliyan 1.4.

Ya kuma ce gobara a cibiyoyin ilimi ta lalata kadarorin Naira miliyan 120, yayin da aka ceto Naira miliyan 200, “An samu gobara guda biyar a kasuwanni, inda aka yi asarar kadarorin Naira miliyan 45, yayin da aka ceto Naira miliyan 90,” in ji shi.

Lawal ya kara da cewa gobara guda 15 sun shafi tashoshin man fetur da iskar gas, inda aka yi asarar Naira miliyan 23.7, yayin da aka ceto kadarorin Naira miliyan 53.

Ya ce kuma an samu wasu gobara guda 15 da suka shafi motoci, inda aka lalata dukiya mai darajar Naira miliyan 70, yayin da aka ceto Naira miliyan 33.

Mai magana da yawun FFS ya danganta yawancin gobarar da matsalar kayan lantarki, tashin wutar lantarki (power surge), adana man fetur ba bisa ka’ida ba da hatsarori.

Gobara
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Hana Al’ummar Cuba ‘Yancin Rayuwa Da Samun Ci Gaba

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Hana Al'ummar Cuba ‘Yancin Rayuwa Da Samun Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.