ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
5 months ago
Gobara

Ibtila’in gobara ta hallaka mutane biyu tare da lalata kadarorin da darajarta ta kai naira biliyan 1.59 a Jihar Bauchi tsakanin Janairu zuwa Disamba 2025, kamar yadda hukumar kashe gobara ta tarayya (FFS) ta bayyana.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar FFS ta jihar Bauchi, Umar Lawal, ne ya bayyana hakan a cikin rahoton kididdigar gobara da aka fitar ga ‘yan jarida a ranar Litinin a Bauchi.

  • Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Bunkasa A Shekarar 2025
  • Kudaden Bincike Da Samar Da Ci Gaba Na Kamfanonin Gwamnatin Sin Sun Ci Gaba Da Haura Yuan Tiriliyan Daya Cikin Shekaru Hudu A Jere

A cewarsa, hukumar ta amsa kiran gaggawa domin ta zo ta kashe gobara guda 167 a tsakanin wannan lokacin, inda aka ceto rayukan mutane hudu tare da kare kadarorin da darajarta ta kai Naira biliyan 2.86 daga lalacewa.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa gobarar ta shafi gine-ginen jama’a da na gwamnati, gidajen masu zaman kansu, cibiyoyin ilimi, kasuwanni, tashoshin man fetur da iskar gas, da kuma motoci a fadin jihar.

Yayin da ya ke yin bayani dalla-dalla, Lawal ya ce gobara guda 10 sun auku a gine-ginen jama’a da na gwamnati, inda aka yi asarar dukiya mai darajar Naira miliyan 23, yayin da aka ceto kadarori da darajarsu ta kai Naira miliyan 855.1.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Ya kara da cewa an samu gobara guda 80 a gidajen masu zaman kansu, lamarin da ya janyo lalacewar dukiya na Naira miliyan 605, yayin da aka ceto dukiya ta kai Naira biliyan 1.4.

Ya kuma ce gobara a cibiyoyin ilimi ta lalata kadarorin Naira miliyan 120, yayin da aka ceto Naira miliyan 200, “An samu gobara guda biyar a kasuwanni, inda aka yi asarar kadarorin Naira miliyan 45, yayin da aka ceto Naira miliyan 90,” in ji shi.

Lawal ya kara da cewa gobara guda 15 sun shafi tashoshin man fetur da iskar gas, inda aka yi asarar Naira miliyan 23.7, yayin da aka ceto kadarorin Naira miliyan 53.

Ya ce kuma an samu wasu gobara guda 15 da suka shafi motoci, inda aka lalata dukiya mai darajar Naira miliyan 70, yayin da aka ceto Naira miliyan 33.

Mai magana da yawun FFS ya danganta yawancin gobarar da matsalar kayan lantarki, tashin wutar lantarki (power surge), adana man fetur ba bisa ka’ida ba da hatsarori.

Gobara
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Hana Al’ummar Cuba ‘Yancin Rayuwa Da Samun Ci Gaba

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Hana Al'ummar Cuba ‘Yancin Rayuwa Da Samun Ci Gaba

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.