Pep Guardiola na shirin barin Manchester City bayan kusan shekara 10 yana jagorantar ƙungiyar.
Rahotanni sun ce kocin mai shekara 55 zai sauka daga muƙaminsa bayan wasan ƙarshe na kakar bana da ƙungiyar za ta buga da Aston Villa a ƙarshen mako.
Tun bayan zuwansa Manchester City a shekarar 2016, Guardiola ya lashe kofuna 20, ciki har da kofunan Firimiya shida da kuma gasar Zakarun Turai ta farko a tarihin ƙungiyar.
ADVERTISEMENT
Tsohon kocin Chelsea, Enzo Maresca, na daga cikin waɗanda ake ganin za su maye gurbinsa.
Sai dai har yanzu Manchester City ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan batun ba.















Discussion about this post