Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sulhunta Hon. Kabiru Alhassan Rurum da Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila, bayan rikicin ya kaure a tsakanin su.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na gwamnan, Mustapha Muhammad, ya fitar a ranar Lahadi.
A cewar sanarwar, gwamnan ya kira wani taro domin sasanta saɓanin da ke tsakanin jagororin siyasar biyu waɗanda aka bayyana a matsayin manyan masu ruwa da tsaki a siyasar Kano ta Kudu.
Da yake magana bayan taron, Rurum, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Rano/Bunkure/Kibiya, ya tabbatar da cewa an warware rikicin.
“An sasanta rikicin kuma yanzu mun sake haɗewa a matsayin tsintsiya maɗaurinki ɗaya, kuma za mu yi aiki tare fiye da yadda muke a baya,” in ji shi.
A nasa ɓangaren, Sanata Kawu Sumaila ya bayyana rikicin a matsayin rashin fahimta.
“Rikicin aikin Shaidan ne, kuma yanzu mun yafewa juna tare da manta duk wani saɓani da ya faru a baya,” in ji shi.














Discussion about this post